4- kishi kenan?

1.9K 373 212
                                    

Haba Haba Haba ghosties, kun kyauta kenan Ace ratio din readers and votes is 5:1,wallahi duk na gani se inji sanyin jikin typing duk yanda na so na muku kuwa. Any way, in tafiya yai tafiya a hakan I will quitely unpublish the story.

Ummu-Abdoul

Sun iso gida ana kiran la'asar, farali kawai su ka sauke aka cigaba da kiciniyar tarbon baki masu zuwa neman aure.

yana da ga cikin al'ada in za'a je tambayar neman aure a daular qahɗanie yin gagarumin biki, dangin amarya kan yanka dabba a bankare ayi balango da shi yayin da su kuma dangin miji za su taho da abinci nau'i nau'i, haka aka yi a gidan Alhaji Bello Yahuza.

Rakumi ya ba masu sana'ar nama aka soke aka gasa shi, su dai a gida an kawo musu shi a gashe ne. Amarya ta ci kwalliya, dangin mahaifiyarta duk sun hallaro na nesa da na kusa kowannensu sai murna su ke.

Fatima ba ta ɓata lokaci ba, tana idar da sallah ta fito sanye cikin doguwar riga yadin yan India (Indian material) ruwan yara (baby color) da ratsin ruwan coffee. Kayan ya fito da ita, ba za ka Kalle ta kace yar shekara ashirin da takwas ba ce don fuskanta sheki yake kamar wata a daren goma sha uku.

An fara taron cikin kwanciyar hankali, masu bincike sun ba da shaida akan Dukkansu nagartattu ne kuma sun dace da juna a matsayin mata da miji kamar yanda akan yi wajen tambaya.

"Tun da an dace, nan da wata bakwai za'a ɗaura aure, zuwa lokacin ta shiga ajin karshe na sakandire" faɗin Alhaji Mus'ab Yahuza waliyin amarya.

Nan duk aka dinga addu'a da fatan alkhairi ga maauratan har ma da iyayensu.

"wai Ke Amina an ce miki ana biye ma binciken kwamitin aure ne, in sun yi na su ku a matsayin iyaye ai ya kamata ku yi na ku, amma kun bar musu su kaɗai, su suka haifa miki. Ko kishiyoyin ki ka biye mawa in har su suka zuga ki" cewa yayan Amina da ke aure a Nijar.

"A'a yaya kada ki musu sharri, ni ce dai na ki yarda zancen su don gani nake bakin ciki su ke min, faɗin farko ita Hajiya Sadiya ta ce wai ai zubaida ta yi kankanta shekara goma sha biyar, ita kuma uwargida Hajiya Hafsa ta bincike ta bullo kin san duk su na da yayyin zubaida a gaban su, ita Hafsa akwai fatima da take babban yar Alhaji sannan da wasu" Ta faɗi tana zumburo baki.

"Toh Allah sa Abdullahin kwarai ne, amma yanda zamani ya canza sai da bincike in ba haka ba ka ɗauki yarka ka kai gidan da za'a kuɗi da ita"

"A'a yaya ayi zato mai kyau, in an yi tunanin alkhairi sai kika ga alkhairi ya tabbata in anyi tunanin sharri kuma se ya bi ka" Ta ce a kufule tana mai jin haushi, a zuciyar ta kuwa mamakin yanda jininta ke mata bakin ciki take.

"Allah baki hakuri ya sanya Alkhairi". Haka dai su ka rabu kowa da abin da yake sakawa a ransa.

***

Farin cikin da zubaida ke ciki baya misaltuwa, don har mamaki dattawa su ka dinga yi yanda yarinya karama ta kosa ta yi aure, wasu ba su ga laifin ta ba don a cewar su zamani ne, da yawa kuma gani su ke akan me za ta bayyana farin cikinta, abin ta shiga zulumin abin da za ta tarar ne.

Tun da aka kamalla take manne da Fatima kasancewar jinin su ya haɗu sosai. Tare su ka yi sallah, bayan magriba su ka yi azkar dinsu har aka kira isha'i, nan su ka gabatar da farali sannan su ka zauna. Take wayar zubaida ya ɗauki kara, cikin mamaki Fatima ke kallonta, don ba ta taɓa sanin tana da waya ba.

"Shine Kaki zuwa, ni fa na matsu in ga fuskan mijina uban ya'yana. Ace har ayi wannan gagarumin taron da ya shafe mu baka zo ba" faɗin zubaida wanda hakan ya sanya ta sakin baki tana kallonta, ba sun ce yaron kawar Ammi ba ne da yake karatu a Ghana, ko da yake kila tana nufin ta daɗe ba ta ganshi ba ne, amma kuma ko shekaran jiya na gansu tare. Duk fatima ke wannan tunanin don kawai sai jikinta bai bata ba. Ba Ta gama farfadowa ba ta ji tana faɗin

BA GIRIN-GIRIN BA Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang