*DAMA TA*
*NA*
*Batul Adam Jattko*
*Mum farhan*
*Hadim fa bata dauki* *Shawaran kiba**Masoyan damata ina kara godiya* 🤝
*Humairan Fandau ta gd*
🌈 *Kainuwa Writers*
*Association*🤝
*20*A general parlour suka yada zango yaran sunata tsalle dan suna son gidan antymum haka suke kiran Hadim saida sukayi sallah zuhr Hadim takira firseh me aikin ta a bangaren kitchen tace "ga yara kuje su fade abinda suke son ki dafa musu muba yanzuba firseh ta amsa da "ok taja yaran suka fice
Hadim bata ajiye wayan ba tace bari nakira my star naji meya kawo motan sa gidaNabil da har lokacin yana fadan askin kan Fandau wayan yayi ringing yana zarowa yaga sunan my one yadaga yace "hutawan ki lfy my Queen
"tace Allah yabarmin my prince na tace fasa meeting din kukayine?
Yace "a a mundan fito hutune na kunna wayan ya akayi ne?
Tace to yanaga motan da katafi dashi a gida
Dasauri yace "gida kuma
tace "eh
Yace "ya akayi kika sani?
Zuciya daya tace "ina gidan fa
Hannun sane yafara kar karwa yabude baki amma yaji mgn ma yagagara
Dabara ya fadu masa yace"ok munzo da amjad ne shine muka fitada tasa nabar nawan.
Tace " ok ai muzone da habiba da yaran kwana ma suka kawomana
Yace "ok sai nazo
Tace "ok my sweet
Yana kashe wayan jiki na rawa yatashi yafita babban parlour part din Fandau ya canza security din kofan duk da yasan balalle bane Hadim tashiga amma yayi hakane saboda tsaro.
Yakalli yanda Fandau take. A sugunne tana nishi nagajiya
yace "jekiyi wanka sanan ki samu sabon towel ki daira kisan yanda zakiyi da Wannan kannaki dan bana san ganin sa me kamadana tsohon baya hude karki kara bari naganshi kiwuce kiyi abinda nasaki inajiranki.
Ya fadi haka yana kwantawa akan gadon yana tunanin meyasa Fandau tafi sauran batan da yasani ne ko wannan tsallen kwadon dan yakarewa jikinta kallo yasata bawai mugunta ba shikan sa yana mamaki yanda akayi gangan jikinsa yake yaudaransa akanta,
Allah Allah yake lokacin tafiyanta yayi ko idan yaga bata kusa zai iya manta ta,
Dan yanajin kunyar ranan da Hadim zatagane yanason wani abu ajikin yarinyan amma idan yatuna da ita taja sai yaji tausayin nata yaragu.
Duk dahaka yana tsoron ranan da zata reskeshi,
Yasauke a jiyan zuciya afili yace Ya Allah kacirewa gangara jikina kwadaituwa da wannan yarinyar kar zuciyata ta kasa daurewa itama takarba da ganan na tozarta a idon Duniya dan babban lefi nayi na auri yarinya bada sanin iyayen taba nima nawa basu sani ba nasan ko shari a sai tamin hakuncin hainci da yaudara danayi,Dukan filo yayi yatashi zaune dan shi yafi ganin lefin gangan jikin sa dan shiya kekai tunanin ta cikin kwakwaln wanshi.
Motsin fitowa tane yadawo dashi daga nunanin ya daka kai yakalli ta daure take da towel kamar yanda yace tayi sai kanta tadaure tamau da wani siriri gele na fakista tsayawa Yayi kallota ya nason yaganta cikin kwalleya da Kananan kaya English weres amma Bata dashi dogayen riguna kawai da fakista hadim tabata a cewar ta ba ado tazo ba karta dauke mata hankalin miji dan komai munin macce idan tayi ado tana kyu
Yana kallon ta ita kuma tasun kuyar da kai tana tsaye a hannu yadan bubuga gadon a laman tazaune ahankali ta zauna ta sake sunkuyar da kai.
Nabil tashi yayi zaune ya nade kafa yasata agaba yana kallon ta hannun sa yasa yadago habanta yakai nasa fuskan dai dai nata a hankali yace "kinyi brush din bakin ki?
Gyada masa kai tayi alaman eh.
Hannansa yasa yaja lips dinta na sama yabude haske masa ido fararen hakoran ta jerarru sukayi bai san sanda yace wow
Dama datti ne yadafar dashi kenan
zuba mata ido yayi yanason yaga munin ta amma sai a sannan yake ganin wasu sirrikan boye na kyunta da mutum bazai iya ganewa ba har sai yanusu hancinta bame tsawo bane kuma bana nen neba ne daidai misali fukanta yanada dan fadi kadan gawani kwantaccen gashi a gaban goshin ta yazo mata har wajen kunnenta sai ka ratse megashi ce dan man askin iya kanta ta shafawa idanuwan ta suna da girma da haske shide Nabil ko jurewa kallon su bayayi Fandau doguwace bata da jiki ban bancin suda Hadim kenan ita farace tas shuwaa amma gajerace ga jiki.
YOU ARE READING
DAMA TA COMPLETE
RomanceLabari ne da baku tab'a jin irin sa ba, matarsa ce bata haihuwa mahaifarta tana da matsana, sai ta sashi ya auri wata yarinya a b'oye babu wanda ya sani daga shi sai ita, akan yarinyar ta haifa musu yara sai ya sake ta, da yarinyar tayi ciki, itama...