1

5.9K 250 10
                                    

*FURUCINA NE*

            *NA*

*BATUL ADAM JATTKO*

'''Marubuciyar'''
*DAMA TA*
*AMFANIN SOYAYYA*
         '''NOW'''
*FURRUCINA NE*

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga  shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

*Page 1*

" Please Madam kar ki damu in sha Allah za ki shiga lfy ki fito lfy mu wannan asbitin aikinmu ba ya samun matsala kin ji? Ki kwantar da hankalinki don kwanciyar hankalinki shi zai ba wa aikinmu karfin gwiwa kin ga a yau ma mata 2 na yi wa Theater nan da sati za ki ji kamar ba ke aka yiwa ba sai de ki sa d'anki a gaba kina kallon sa ki ci kaji ki ci ragon suna".
Dr Fanna ta k'are maganan tana mata murmushi
Hajiya Halima ta yi murmushi cikin azaban ciwo ta ce "Dr ba wani Dan Adam da ya isa guje wa kaddararsa a jikina nake jin ba zan rayu da abin da zan haifa ba, amma don Allah Dr Fanna ina neman  alfarma a wajenki dan Allah idan Allah Ya sa ban tashi ba  ki rike min d'ana amana kar ya yi maraici yanda ni na yi kuma ina son ki auri Addulsamad mijina ni ban san asalina ba an ce wai hatsari mota muka yi da Babana shi ya yi loosing  memory wanda har yanzu bai dawo hayyacinsa ba iya sunansa kaɗai ya sani yake iya fada kullum idan na ce masa Baba ina ne gidanmu su waye danginmu ba ya magana sai de ya ce *Nasuru*  ni kuma fuskata ta b'aci aka canza min wata dan da banma san asalin fuskata ta da ba
a gidan su Abdulsamad na samu kaina kuma shi ya zama mijina.  Ba wahalar da ban yi ba wajen neman dangina ga shi har ina shirin barin duniya ban san ni wacece ba, ban san dangina ba.  Babana bai dawo hayyacinsa ba kuma motan da muka yi accident  da shi ance  ya kone ba asamu wani bayanai a ciki ba. Ina tausaya wa abin da yake cikina don shi ma na san zai yi rayuwa cikin rashin uwa duk da yana da nagatarcen uba kamar Abdulsamad. Ki ceci rayiwan d'ana ta hanyar  auren ubansa dan idan na san a hannunki na bar shi ba ni da sauran damuwa, Dr Fanna kina da tausayi da amana duk da ban san halinki ba, amma ki min alk'awarin za ki auri Addulsamad yana da kirki haka danginsa ma suna da kirki amma hankalina ya fi kwanciya  dake"

Juyawa ta yi ta kalli inda mijin nata yake da ganin yanda ya hade fuska ka san ba ya son maganganun da take yi.
Murmushi ta yi ta sake damk'e hannusa ta ce " Ya Abdul na san ba ka son wannan maganganun nawa amma na rasa me ya sa nake yin su nima. Kuma  na san ka amince za ka auri Fanna ko da ina raye ne ina son ka dauki Fanna a matsayin Halima ka ga kai ma ka sha cewa muna yanayi da ita. Abdulsamad ka yafemin idan da gaske ne scanning din da akamin namiji ne abinda zan Haifa kasa masa sunan Babana *NASURUDDEEN* idan macece Halima dan Allah ka ce wa dukkan danginka su yafenin, idan Babana ya warke ka ce masa ya yafe min. Ina son sa  haka  ina son mahaifiyata idan ka ganta ka ce na rayu da son ganinta  Abdul Ina SON KA INA SON KA ,  INA SON KA AURI FANNA SHI NE FANSAR SOYYYAR DA NA MAKA YA ABDULSAMAD ka yafemin"

Cikin rikicewar murya da tsorata da al'amuran nata ya ce
" Halima amma mun gama duk wannan maganganun tun a gida ko? Da kin bari an fara aikin nan da yanzu an gama ma." 
Dr Fanna fita ta yi dan wani irin kuka ta ji yana shirin kwace mata da sauri wata  Nurse  ta bi bayanta 
ta ce
"Dr idan ta k'ara wasu minutes  za a iya samun matsala fa".
Ficewa ta yi a Theaterroom gabadaya ta yi office dinta nurse Zainab na bin bayanta. Daukan wayanta ta yi akan Table  amma ya kubce zai fadi da sauri Zainab ta tare ta ce" Dr wa za a kira miki".
Cikin kuka ta ce "Dr Husaina ko Dr Hafsa".

FURUCI NA NEWhere stories live. Discover now