K'arshe

2.4K 66 9
                                    



Bayan sati d'aya da faruwar haka:- Abakar da matansa suna zaune lafiya k'alau saidai har yanzu basu sake da juna ba, musamman Maryamah da take bala'in tsoron Fad'ime, wani lokacin har ita ke cewa ''ki saki jikinki, ai nima yayarki ce'' amma duk da hakan tsoron ta take, kuma ko da wasa bata bari Abakar yazo kusa da ita, indai Fad'ime na gidan ta dinga guje masa kenan. Dr. Sulaimana kuma yak'i d'auka k'iran wayan kowa daga gida Damaturu dan bai son ace yazo ya d'auki Hamrah.
Yafi son in ta horu ta dawo da kanta kamar yanda ya fad'awa abokinsa Abakar da yace ''bai dace ka barta ta tafi ba, ka dawo da ita indai akan Maryamah kayi haka komai ya wuce'' shi kuma yace bai yadda ba sai tayi hankali. Kallonsa kawai Abakar yayi bai sake tanka sa ba.
Yau Abakar da iyalinsa sun tashi cikin shirin zuwa Godil kasancewar Maryamah bata tab'a zuwa ba tunda akayi auren haka shima Abakar bai tab'a zuwa ba, yau kimanin shekara bakwai rabon ta da can, taci kwalliya ta ci ado ta sa hijabinta.
Tana fitowa suka ci karo da Abakar da yake shirin shigowa, komawa tayi ya rufe k'ofar yasa makulli yana kallonta, fuskar nan a had'e ba daman tayi rigima. Matsowa yakeyi kusa da ita tana komawa baya har suka isa bango sannan tace ''ni me nayi ne?'' Ya kamo hannunta ya matse sai da ta saki k'ara sannan yace ''babu inda zaki je tunda gudunah kikeyi'' hawaye ta fara zubarwa tana cewa ''ni ba gudun ka nakeyi ba tsoron matarka nakeyi'' matsowa yayi dab da ita numfashinsa na sauk'a akan fuskarta, ita kuwa ta runtse ido tana Allah-Allah ya tafi kada Fad'ime ta gansu a haka. Ji tayi yace ''in munje mun dawo raba kwana za'ayi ma kowa ya huta'' Ya cize mata hanci yana cewa ''ko in gutsire hancin nan gaba d'aya'' turo baki tayi zata yi magana ya toshe da nasa.
K'wank'wasa kofar da akeyi ya bata damar ture shi tana cewa ''ina zuwa Anty'' ta sa kai zata isa wurin k'ofar ya janyota ta fad'o jikinsa, k'ok'arin kwace kanta takeyi yak'i saketa, rantsuwa ta fara masa akan ta yadda a raba kwanan in sun dawo sannan ya k'yaleta ta fice ya bi ta a baya.
Fad'ime ce zaune a gefen mijinta, Mama Zainaba da Maryamah a baya, Zahra k'arama kuma tana gun Mama Zainaba. Maryamah ce ta nuna musu hanyar garin har suka isa k'ofar gidan da misalin k'arfe hud'u na yamma. Maryamah ce ta shiga tare da sallama da murnarta, Amty Babbe ta fara gani a tsakiyar gida tana kwance akan tabarmarta kamar yanda ta saba. Tana ganin Maryamah ta mik'e da murnarta tana cewa ''Maryamah ke ce?''.
Tuni ta fashe da kuka tana cewa ''ashe zan sake ganinki? Kwana biyu Sulaimana bai zo ba nayi ta tunanin ko lafiya ashe kina tafe?'' Ganin su Fad'ime tayi da Mama Zainaba a baya tace ''ashe da mutane kike? sannunku da zuwa sannunku'' ta d'auko tabarma a d'aki ta shimfid'a musu, Maryamah sai kallon gidan take dan ba haka ta barshi ba, abun mamaki sai gani tayi Amty Babbe ta bud'e fridge ta d'auko ruwan sanyi ta ajiye musu, a ranta tana cewa ''wannan aikin waye? Sulaimana?''.
Ta d'auke tunanin suka gaisa sannan ta fad'a mata su waye ne mama Zainaba da Fad'ime. Ita ta shigo da Abakar Amty Babbe ta mik'a masa kujera ya zauna sannan suka gaisa.
Maryamah tasha mamakin Amty Babbe dan yanda take magana kamar tasan komai, harda cewa ''ina miki murna Maryamah''. Ta fad'a musu Sulaimana ne ya sa aka buge gidan nasu aka musu na bulo, d'akuna hud'u da falo da toilet irin na zamani. Sunyi hira sosai sun zagaya gidan sun kalla sannan suka baje a tsakar gida aka cigaba da hira.
Sunyi kwana biyu anan sannan suka wuce Damaturu bayan Abakar ya musu sha-tara ta arzik'i, Amty Babbe harda hawayenta, Ammi Malud ma yayi murna sosai da ziyarar da suka kawo musu yayi musu fatan alkhairi.
Sai da sukayi sati biyu a Damaturu sannan suka tattara suka juyo Kaduna harda Hamrah ba tare da sanin Dr. Sulaimana ba. Da isar su kawai Abakar ya k'irasa a waya yace yana gidansa, shigowarsa ya gansu sun shantake a falo suna hira, gaisawa kawai sukayi Abakar yace ''mu wuce koh'' suka tashi suka fice ko rakiya Abakar yace ya hutar dasu.
Hamrah ta bada hak'uri kuma ta tabbatar masa bazata sake yin abu makamancin haka ba. Dama yayi missing d'inta tuni ya rungume abarsa komai ya sauya. Ranar ba shi ya d'auko yara daga islamiya ba sawa yayi a dawo dasu. Rayuwa mai dad'i suka bud'e cike da jin dad'i.
Kafin dawowar su Abakar ya sa an gyara d'akin da Maryamah zata zauna, ya canja wa kowa kayan d'aki dan ya k'uduri niyyar yin adalci tsakaninsu. A ranar kuwa da dare ya tara su a falonsa yayi musu nasiha sannan aka raba kwana. A wurin Fad'ime ya fara kwana bayan kwana biyu ya koma d'akin Maryamah.
BAYAN SHEKARA HUD'U, Maryamah zaune tare da Zahra tana koya mata karatun islamiya Fad'ime ta fito da yaro a hannunta tana cewa ''Kwaiseh yaron nan naki akwai rigima, wai yaro d'an wata uku har yasan hannun uwarsa, tunda na d'auke shi kuka yakeyi'' Maryamah tayi murmushi sannan ta karb'e shi tana cewa ''Abuyi Halali(babana halaliya na) kenan, ai kunzo a daidai dan mun gama saura na boko zaki koya mata''.
Zahra ta kalli Fad'ime tace ''mama me yasa Anty kwaiseh bata yi min na boko, bata iya ba koh?'' Fad'ime ta janyo ta jikinta tana cewa ''ai kowa da fannin da ya karanta, kinga ni ban iya islamiya ba ita ta iya koh?'' Zahra tace ''naji dad'ina, malamin islamiya ma yana cewa wanda yake koya min karatu malami ne nace masa a'a antyna ne kuma yace na iya sosai dan rannan abinda ya tambaya na bashi amsa wai aji biyar akeyi kuma na bada amsa'' Fad'ime tace ''toh kin gani, babanki kuma in an baki abun gini a school shi zai miki dan civil engineering ya karanta'' Zahra ta tafa hannunta tana cewa ''ni zan zo na d'aya a aji tunda kowa ya iya abunda ake mana a makaranta'' dukansu suka yi dariya. Abakar da yake danne-danne a laptop nasa cewa yayi ''in an koya miki kin iya kenan ko? Dan ba su zasu miki exams ba'' tace ''Abba ai inayi, kuma anty ta sani koh'' ta fad'i hakan tana kallon Maryamah, tace ''eh ai daughter Zahra na da ilimi'' murna ta fara yi tana cewa ''yes'' harda rawarta.
K'arshe.
Alhamdulillah, nagode Allah mai kowa mai komai da ya bani ikon kammala littafina. Inason k'ira ga 'yan uwana mata musulmai, mu rik'i addini kuma mu fifita shi akan duk wani ilimi, in mace batayi boko ba kada ku rainata ku k'ask'antar da ita, tabbas ilimin boko na da anfani a rayuwarmu ta yau amma ku sani ba sai anyi boko ake succeeding in life ba. Duk k'arancin ilimi zai anfaneka watan watarana. I dedicate dis book to all my fellow muslim sisters, i love you all, Allah ya kare mu ya d'aukaka addininmu(ameen)
Godiya ta musamman ga:-

Nagarta writers association

Excellent writers

Gorgeous writers

Hausa novel group 1,2 nd 3

Rukiee sadau grup, Nuceey grup, Rufaida umar grup, dandalin hausa novel, gidan littafai, readers, fancy grup nd mermue home of novella da duk grup d'in da banyi mentioning ba ban manta daku ba kuna raina. Thank you oll. Nd to my facebook dear members ina godiya sosai Allah ya bar zumunci... na barku lafiya, with bunch of love

Kwaiseh MaryaamahWhere stories live. Discover now