MATAR ABDALLAH 09

6.7K 424 54
                                    

💧💧 *MATAR ABDALLAH.!*💥
                   True Life Story.!

                              💥

*©HASKE WRITER'S ASSO.💡*
Home of expert & perfect writers

*MALLAKAR: FEEDOHM💞*
   *Wattpad:Feedohm*

*09*

        *This Snippet goings to DarlingSlimzy and PharmLawysat.I pray to Allah to expose your enemies,i pray that Allah deny them what they want, humiliate them, let them see no peace anywhere in this world, protect all of us that need protection and guides all our affairs. Amin*

***
  Hayaniyar da Muhibba tajiyo yasata fitowa da sauri, Tun a falo ta fara  jiyo kamar muryar Maryama kuma ta tabbata babu abunda bara ya iya faruwa ba idan maryama ta iske Abdallah. Ta sani sarai Maryama batta da hakuri kuma bata jure komae k'ank'antar wulakanci da cin mutunci daga gurin kowa, balle ma ace Muhibbarta aka tab'a..

  Cak ta tsaya ganin Maryama rike da k'walar rigar Hasna yayin da Abdallah ke k'ok'arin rabasu, muryar maryama taji tana fad'in " Ance maki juyar ko ba ita bace? ki fad'a man idan akwae shegen da yasa ki yanke mahaifarki? uban wa ya sani ma ko dan baki haihuwa yasa Abdallah auren Muhibbar."

  Cikin k'yarma ta fara kiran sunan "Maryamar."

  Ita kam ko saurarenta bata yi ba ta cigaba da fad'in "Munafuki da dad'in baki ya saye zuciyar k'awata ashe duk munafurcine."

  Kuka ne ya ci k'arfin Hasna ta kai hannu ta kaiwa Maryama duka a kai ta goce da sauri.

   Muhibba ta k'araso tana kuka tana jan Maryama"Dan Allah ki bari Maryama banna so."

  "Barni Muhibba."Ta fad'a a hargitse

  "Na shiga uku, dan girman Allah ki zo muje maryama ki daina nace ."Ta k'arashe maganar cikin matsanan cin kuka.

  Gani tayi Maryama ta zub'e k'asa yadda kasan yar bori sae juyi take tana birgima tare da wata irin kuwwa tana fad'in "Sae ni Sarkin Aljanu zanzakitu, me yasa aka b'atawa god'iyarmu rayi? ba zamu yarda ba, sae mun kasheku..Hoooo."

  Baya Abdallah ya ja yayin da Hasna ta koma bayanshi cike da firgici,Ita kam Muhibba iya rud'ewa ta rude don bata tab'a tunani ko jin ance Maryama na da aljanu ba sae yau,"to ina ta samesu? na shiga uku kar dae ace sanadina Aljannun maryama suka fara bayyana."

Adadin kukanta ya karo yayin da tayi ta maza ta duk'a ta rike maryama gam tana tofa mata addu'a

  "Duk ke kika janyo komae Muhibba."Abdallah ya fad'a sae raba ido yake

  "Munafuki ba ita ta janyo ba kaine.! duk abunda kuke muna binku a baya kuma muna kallonku! harta abunda kuka bata gurin party mune muka cinye bayan kun tafi, kuma sae mun kasheku."A ka fad'a cikin wata irin razanannar murya

  "Sae mun kashe ku idan ba'a bata hakkinta ba."A ka kuma fada cikin tsawar gaske

  Sosae su duka suka razana amma hakan baisa Muhibba sakin Maryama ba sae ma k'ara rik'eta da tayi duk da tana tillar da ita gefe guda

  "Hoooo Baku ji bane..Ina lefenta.?

  Cikin k'yarma Abdallah yace "Wallahi lefenta nanan kuma za'a bata hak'k'inta don Allah kuyi hakuri."

  Hasna kam da gudu ta fad'a d'aki ta shige can k'uryar gado ta nannad'e don har ga Allah bata taba ganin aljanu sun taso ba kuma tana da bala'in tsoro

  Bin bayan Hasna yayi cikin k'yarma yana fad'in "Muhibba dan Allah ki mata addu'a su tafi,sanna ki basu hakuri ki kaita d'akinki bara na dauko lefen na kawo sae a raba maku k'wana, ai shikenan ko.?

MATAR ABDALLAH..Where stories live. Discover now