62

7.5K 501 388
                                    

_*RASHIN SANI.......*_


*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_

'''Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh'''


6⃣2⃣


Cikin zunzurutun tashin hankali Khulud ke kallan Sanah tana girgiza mata kai,
jikinta na rawa da kerrrrma ta nufi Sanah dake tsaye idonta kanta,
ta dafa kafad'arta tace " no..! please karki yi min haka dan girman Allah,
ta fad'a yadda babu mai jin abinda take cewa,
murmushi tayi tare da cewa " dole nayi miki haka,
lokacin dana so rufa miki asiri ni tuna min nawa kikayi,
lokacin dani na nemi taimakonki k'in taimako na kikayi,
" wai yama zakice karka nayi miki haka....!?

"So kike nayi ta zama da auren wanda bai sani ba a kaina.....!?

" Ko so kike yi ni rayuwata ta k'are a haka ba tare dana mori komai daga gare ta ba....!?

"Ko kina nufin nayi ta zama da aure har k'arshen rayuwata....!?

" Dan girman Allah ki rufa min asiri,
wallahi a yau zan saka shi ya sake ki,
amma dan Allah karki tona min asiri,
" kiyi hak'uri Khulud hakan ita kad'ai ce mafita,
hakan ne kad'ai zai kawo k'arshen komai,
ya kuma bayyanar da gaskiya,
ta yadda kowa da zai san meke faruwa a tsakanin mu,
duk irin shak'uwar dake tsakanin d'a da mahaifi amma Dide da Juju kasa tantace Khulud d'in gaskiya suka yi،
haka ma Abbu da Mamu kwata-kwata basu gane Sanah ba,
cikin rawar murya Abbu yace " wai meke faruwa ne....!?

"Ke wacece، daga ina kuma kike....!?

Ya fad'a yana kallan Sanah,
murmushi tayi gami da kallan Sir Moli،
dake tsaye hard'e da hannuwanshi a k'irjinshi,
yayi mata alama data cire fuskar da voice maker,
babu musu Sanah ta cire fuskar da voice maker d'in,
ai sai lokacin suka k'ara shiga cikin rud'u da tsantsar tashin hankali,
saboda tsabar tsoro Jaddah bata san sanda ta soma hawaye ba,
Halan ta kalli Mamu tayi mata alama da kinga ni ko...!?

Itama Mamu Abbu ta kalla wanda ke tsaye tamkar an dasa shi,
gumi ya gama jik'a shi sharkaf,
Dide kam shiru yayi ya kasa koda motsi haka ma Juju,
Sanah tayi murmushi had'i da cewa " yau in sha Allah gaskiya zatayi halinta,
sirrin b'oye zai fito fili, kowa zai san gaskiyar al'amari,
cikin nutsuwa Sir Moli yayi gyara murya,
" dan Allah kowa ya zauna akwai sauran bayanan da zamu tattauna,
jiki babu kwari duk suka zauna,
yayinda Ziyad ya rarrafa ya rab'e jikin Halan,
Hanash ko motsi ya kasa yi balle ya samu damar zama,
Sir Moli ya kalle shi yace " dan Allah ka zauna Hanash...!
gumi na ketowa Hanash yace " cigaba please,
yayi kamar wani sokoko,
ganin yanayin dayake ciki yasa Sir Moli mai da kanshi ga sauran jama'ar,
had'i da yin gyaran murya a karo na biyu,
ya d'aga diary d'in Papu yace " wannan shine littafin aje muhimman bayanai na Marigayi Alhaji Waseef,
wanda a turance ake kira da diary,
mamallakin littafin Marigayi Alhaji Waseef Papu yayi rubutu kamar haka,
_" ni Waseef na d'aura auren d'ana Hanash Waseef,_
_da 'yar aminina Sanah Hamraz na d'aura musu aure a yau ranar 10/ May/2018 wanda yayi dai-dai da hijira ta 1439 5 ga watan Shawwal,_
_akan sadaki naira dubu d'ari 100k,_
_a gaban shaidu mutum shida bayan ni waliyin Sanah,_
_da Malam Udu driver na wanda shine yayiwa Hanash waliyanci,_
_bayan na tabbatar da Sanah ta yarda ta kuma amince,_
_shima kuma Hanash ya amince akan zan aurar dashi,_
cikin rud'u Hanash ya sunkuya gami da dafe kanshi yana tuna lokacin da Papu ya kira shi kan maganar aure.

Shekara d'aya da watanni da suka wuce a baya

Bayan Khulud da Sanah sunzo kan maganar auren Hanash da Sanah,
Papu ya kira Hanash parlor'n shi,
Papu da Hanash zaune cikin parlor,
Papu ya kalli Hanash yace " gaskiya Hanash hankalin mahaifiyarka ya tashi sosai akan rashin haihuwarka,
dan haka ina son ka k'ara aure,
a razane Hanash ya d'ago kanshi ya kalli Papu tare da cewa " aure fa kace Papu....!?

RASHIN SANI......!!! Where stories live. Discover now