HM - 08

3.7K 295 12
                                    

HAMEEDA POV.

Kamar kullum yau ma gaban window take tsaye tana kallon harabar gidan da kuma masu kai da kawo a harabar.
  A zahiri harabar gidan take kallo, amman a badini, hankalinta yana wani gurin ne daban, dalilin da ya sanya Zain ya juya mata baya take nema, irin rayuwar da suka yi a gidan take tunawa, ta yi marmarin irin kulawar da yake bata a baya, tana kaunar zaunawa da suke suna fira da juna.
  Amman komai da canja mata? Mutumen da a duniya yafi kowa tsanar ganin hawayenta a yau shine yake kwadaituwa da saka ta kuka, mutumen dake kokarin yaye mata damuwarta a yau shine damuwarta take sashi farinciki.
  Ta kasa yarda da komai, yau gobe burinta ya kasa ciki, ta kasa samun natsuwar aure kamar yadda ko wace mace take samun natsuwa a gidan mijinta, saboda ta hana kanta haihuwa, a yanzu kuma tada fito tana jiransa sai ya dauki kiyayya ya dora mata? Har gobe ganin take Anty Ummi ce ta shiga tsakaninta da shi, domin a da ba haka yake mata ba, gani take kamar itace ta saka ya auri Yayarta a maimakonta, bayan kuma ita tafi dacewa da shi, ta kasa yarda cewa Zain baya sonta.
  Juyowa tai tana fuskarta cikin dakinta, but still jikinta na jingine da ginin gurin, a hankali ta sauke numfashi.

“Wannan ce kadai damar da nake da ita a rayuwata, itace kawai hanyar da zan iya gusar da kiyayyata a zuciyar Zain, ina son mu koma kamar baya, ina kwadayin ka zama abokin rayuwata na har a bada Zain”

Ta furta a hankali sannan ta tako cike da kasaita ta karaso gaban kujerarta dake gefen godonta, har zata zauna sai kuma tai tsaye tana ta tunani.
  Yadda zata gyara alakarta da Zain take tunani, a ganinta har gobe Zain yana kaunarta kawai dai an shiga tsakaninsu ne.
   Kwankwasa kofar dakin akai, hakan yasa ta dago kai ta kalli kofar, bayan wasu yan seconds Abida ta turo kofar dakin ta shigo bakinta kumshe da sallama, kanta a kasa karasawa tai gaban Hameeda ta risina.

“Allah ya taimakeki Mai Martaba yana nemanki”

Kallon rashin fahimta da mamaki tai mata.

“Kin san dalilin kiran?”

“Ban san komai akai ba ya shugabata”

Yawun bakinta ta hade, ta soma takawa a hankali har ta isa gaban wardrobe dinta ta bude ta dauko mayafi ya rufe kanta sannan ta nufi kofar fita, zuciyarta na zillon rigan kafafunta. A iya saninta Mai Martaba baya fada a yanzu, kuma idan har wani hukunci zai yanke ko wata magana data shafi iyalinsa a falonsa na cikin gida yake zartarda komai. Kai tsaye part dinsa ta nufa tana kai hannu ta bude kofar falon farko sai gabanta ya soma faduwa.

“Assalamu Alaikum”

Tayi sallamar ne tana kokarin danne zuciyarta, yan matan Mai Martaba ne suka amsa mata, wato Sisters din Zain, cikin falon ta tana karewa duk wanda yakr cikin falon kallo kasa kasa, Hajiya Hadiza ce a kujerar dake kusa da ta Mai Martaba, sai Hajiya Maryam na binta, da Hajiya Zarah dukansu Matan Mai Martaba ne, Dada  Yalwa na zaune a kujerar data saba zama a duk lokacin da irin hakan ya samu.
  Tun da ta zauna bata sake dago kai ta kalli kowa ba, wannan dabi'ar na daya daga cikin dabi'un da Mai Martaba yake so, yana cikin dabi'un da ake yabon Hameeda da su har ake ganin tafi duka yaran sarkin kunya.
  Gyara muryar Mai Martaba yai, wannan yasa hankalin kowa ya koma kansa kenan, ciki har da Zain da zuciyarsa take can asibiti.
 
“Zain...”

Mai Martaba ya kira sunansa, a natse ya dago ya kalli Mai Martaba.

“Mi Hameeda tai maka?”

Kallon Hameeda yai yaga kanta kasa, sai ya kalli Dada Yalwa kamin ya maida dubansa gurin Mai Martaba.

“Allah ya taimaki Mai Martaba, bata min komai ba”

Dada Yalwa ta tari numfashinsa.

“Bata maka komai ba, zaka ce ta daina shiga sasshen ka? Ta daina bi inda zata ganka? Kace ka tsaneta? Ba wannan dalilin yasa tace zata bar gidan ba, saboda kana nuna mata banbance da sauran kannenka, kuma ba kowa ba ne sai wannan Ummi ita take zigashi a komai, har cewa yai ba zai kara kaunar Hameeda ba a rayuwarsa”

HAFSATU MANGAWhere stories live. Discover now