Ƙ page 34

495 77 5
                                    

       *ƘADDARAR RAYUWA*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡

Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on wattpad@zeeyybawa."

Page 34

      Washe gari dady ya fita da wuri dan haka sadam bai samu yayi magana dashi ba,  wunin ranar haka sadam  yayi shi jikinsa gabaƙi ɗaya babu ƙwari, har mummy sands ta afahimci hakan amma bata tanka masaba saboda tace duk ranarda abunda yake damunsa yayi tsamari taji tunda har yaƙi faɗa mata abun bai dameshi bane, daga ƙarshe wunin ranar a gidansu najeen yayi shi najeeb yaci gabada bashi shawarwari yanda zai  ɓullowa al'amarin da yanda zaiyiwa dady magana ya ɗauki maganarsa da muhummanci sai dare yadawo yana son ganin sawwama amma bai samu yajeba, saboda yafiso har sai randa yayiwa dady magana dady ya amince tukunna zaije wajanta da gwarin guiwa, sadam bai samu ya zauna da mahaifinsa yayi masa magana dashiba saboda da wuri yake fita aiki sannan kuma yadawo da dare, dan haka ya yanke shawarar cewa zai bari a weekend ya sameshi d azancen, sannan kuma har wannan lokacin bai ƙara komawa wajen sawwama ba amma kullum suna waya akai-akai duk yanda yakeson ganinta haka ya haƙura,

Ranar friday haka ya wuni da faɗuwar gaba saboda washe gari yake sanya ran yiwa dady magana saboda ya gaji da wuni da kwana da taraddadi cikin ransa,
      Bacci kaɗan sadam yayi aranar gani yakeyi kamar safiya bazata yiba saboda yanda ya ƙagu yayiwa mahaifinsa magana, tunda yaji wani daga cikin ƴan uwan baba sun fito neman aurenta ya gigita da zullumi take kwana aransa, zuciyarsa bazata iya jure rashin sawwama ba,

sai bayan yyi sallar asubahi sannan bacci mai nauyi ya ɗaukeshi, bai farkaba sai wajan ƙarfe goma 10:00am yatashi toilet yawuce yayi brush yayi wanka ya fito ya sanya kaya ya fita zuwa palour, qannensa yasamu a palour suna zaune hassna tace yaya sadam breaksfast ɗinka yana man diining mummy tace  idan kafito a gaya maka,

Toh yafaɗi sannan yawuce dining bai wani tsaya cin abinci sosai ba saboda yanda hankalinsa duk baya jikinsa ɗakin dady ya wuce kai tsaye bayan yayi sallama ya tsaya bakin ƙofa mummy dake ciki tace shigo mana sadam,

Toh sadam ya amsa sannan ya sanya kansa ciki, a kishingiɗe ya samu dady yayinda mummy take gefensa ga dukkan alamu taɗi takeyi masa kuma yana jin daɗin taɗin dan yanda annuri ya nuna a fuskarsa,  ƙarasawa sadam yayi ɗan kusa dasu ya zauna akan guiwowinsa ina kwana dady yafaɗa yana kallon mahaifinnnasa dady ya amsa fuskarsa sake cikeda annashuwa yace lafiya ƙlau sadam katashi lafiya?

Lafiya ƙlau sadam ya ansa sannan yace mummy ina kwana? lafiya son harka tashi? Eh mummy natashi,
Shiru sadam ya zauna yayi yarasa ta yanda zai furta zancen dayake bakinsa,

Dady ya tashi ya zauna ganin sadam a zaune yasan magana yake tattare dashi lafiya sadam naga kamar kana son yin wata magana kuma kayi shiru karkaji komai faɗa kawai,

  Kallon mummy yayi yace mummy dan Allah zamuyi magana da dady, zaro ido mummy tayi tace mai kake nufi kenan?

Sun kuida kai sadam yayi yace da dady kaɗai nakeson yin magana,
Da mamaki mummy ke kallon sadam wato har akwai maganarda zaiyi da dadynsa batareda ita ba?

Murmushi dady yayi yace toh mummy d'an bamu waje zamuyi magana da son ɗinki dady yayi magana cikin zolaya, kyaɓe baki mummy tayi ta miƙe tana faɗin tunda ba'a gayyatarmu a cikin zancen ai koba afaɗa ba zamu tafi, mummy tayi ta waje sadam ya bita da kallo, ta fita da kusan 2minute amma sadam baice komai ba,  dady yace sadam kai nake sauraro, waiwayawa sadam yayi ya kalli ƙofa sai yana kallon kamar mummy bata tafi ba miƙewa yayi yaje ya leƙa ƙofar, ganin bata waajn ya sanya yaja ƙofan ya sanya mata key yadawo kusada dady ya zauna shi dai dady kawai ya tsaya yana kallon ikon Allah bai san wace magana bace haka da har sai an kulle ƙofa kafin ayita,

Zaunawa sadam yayi daf da dady yace dady dan Allah wata alfarma nake nema awajanka, dady ka taimaka ka tausayamin ka dubi wannan zance da zanyi maka da kyakkyawan tunaninka, dady ka duba zancenann da muhummanci kamar yanda kowani lokaci nake ɗaukan all'amurana da muhimmanci,

Murmusawa dady yayi yace In sha Allah can yiwa lamarim kyakkyawan fahimta sadam kai dai yanzu karkaji komai faɗamin wace maganace?"

Dady ni dai dan Allah kayimin alqawarin bazaka ƙi zancen da nazo maka dashi ba, girgiza kai dady yayi yace bazanyi maka alkawari ba sadam saboda bansan zancen ba amma nayi alƙawari zanyi iya ƙoƙarina nayiwa zancen kyakkyawan fahimta yanda bazan cutar dakai ba, yanzu inajinka faɗamin abunda ke tafe dakai kabar wannan noƙe-noƙen, dady dan Allah kayimun aure wallhy aure nakeso yafaɗi zancen da sauri kamar wanda zai sanya kuka,

Dady bai san lokacinda yafara dariya ba yace sure kakeso sadam? Sun kuida kai sadam yayi yace eh, jijjiga kai dady yayi yace sai yanzu na fahimci dalilin dayasa bakaso mummynka taji zancen, amma sadam kasan yanda za'a kaya da mummynka akan wannan zancen koh?

har yanzu kallon ƙaramin yaro take maka wanda bai isa aureba, nasani sadam yace sannan yadaura da fadin sanin hakan yasa na sameka dady saboda kai kafi kowa fahimtata kuma nasan idan har ka amince to zaka iya shawomin man mummy,

Nisawa dady yayi yace har indai ta wajena ne banda matsala sadam saboda ko ni lokacin dana auri mummynka ban kai age ɗinka ba, kuma na riƙeta mun zauna lafiya idanba ɗan abunda ba'a rasawaba bazata ce maka ga wani mummunan abunda nayi mataba, amma inaso kasani na auri mummynka tana sona insa sonta, yanzu  kai akwai wacce zaka kakesone?har kakeson aurenta?"

Gyada kai sadam yayi yace eh dady, nisawa dady yayi yace nafarko sadam kai ba aiki gareka ba, mummynka baso takeyiba kana kallon ahaka zaka samu farin cikin da kakeso?

nan da nan idon sadam suka cicciko yace dady dan Allah ka taimaka wallhy yarinyar nan tun bata kai haka ba nafara zuwa wajanta babanta ya hanata kula kowa hatta da ƴaƴan ƴan uwansa sun nuna suna sonta babanta ya hana saboda yanaso yadawo mutumin kirki mai cika maganarsa, dady dan Allah karkace a'a zan zama mayaudari, bazasu ɗaukeni mutum mai gaskiya ba ko kaɗan mutumcina zai zube idanuwansu, nima kaina cikin zuciyata can zame me kallon kaina matsayin maci amana, dady ina fada maka hakane saboda nasan zaka fahimceni kuma a halin yanzu bbu amfanin ɓoye maka komai,

Jijjiga kai dady yayi yace naji amma mai yasa abaya ka ɓoyemin? Saboda ina tsoron yanda mummy zata ɗauki zancen sadam tafaɗi,

Toh sadam nidai yanzu bazance komai ba sai dai Allah ya za6a mana abunda yafi alkhairi zanyi ƙoƙoari har naga nacika maka burinka, amma kasani kada ka saka hope akaina da yawa ka ɗauki alamuranka da miƙawa ubangiji shine zaiyi maka magnin komai ba niba,
tashi kaje idan zaka wuce kacewa mummynka inason magana da ita sai naji ta bakinta saboda tanada hakki akanka bazan taɓa yimaka aure ba tareda amincewarta ba."

* FITATTU BIYAR NA KUD'INE.*

*FEEDOHM - SILAR WAYE?*
*ZAINAB BAWA- YARIMA FAYAD.*
*ZEE YABOUR - DR MUHRIX.*
*HAJJA CE - ANNURIN ZUCIYA.*
*NANA DISO - GIMBIYA SUHAYMA.*

LITTAFI BIYAR AKAN___500,
IDAN HUDU KIKE SO___450,
IDAN KUMA UKU NE___400,
IDAN BIYU KIKE SO___350,
IDAN KUMA D'AYA KIKE SO 200.!

TURA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT D'IN.

3126584401 FIDDAUSI MUSA FIRST BANK TARE DA SHAIDAR BIYA A 08036953516

KO KUMA.

ACCOUNT NUMBER:-   0003075326  ZAINAB M BAWA
Jaiz bank SHAIDAR BIYA TA 08161146563.

*KO KATIN MTN TA WANNAN LAMBAR 07065283730 TARE DA SHAIDAR BIYA.*

*SANNAN MUYI ADDING D'INKI A FITATTU GROUP🌹...*

Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,

Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.

Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."

✔️ote
Comment
Follow
Share plss

To be continued
Zaynab Alabura

ƘADDARAR RAYUWAWhere stories live. Discover now