K page 56

341 50 1
                                    

*ƘADDARAR RAYUWA*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡

Written by
              zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
              wattpad@zeeyybawa."

          Muna saida kaya, material, laces, atampha, shadda, takalma kayan kitchen da sauransu akan farashi mai sauki siya daya ko sari,
Alarabee's hair cream is available pcs, cotton, half cotton, yana gyara gashi, cire dandruff, hana karyewar gashi, yana softening gashi, yana saka bakin gashi yana saka cika da tswon gashi🥰  masu bukatar kaya ko hair cream ku tuntubu wannan lambar 08161146563

Page 56

  Kusan kullum ne sai sadam yakira sawwama a waya  wani sa'in sukan dauki lokaci mai tsawo  suna hira wani lokacin kuma sukan gaisane kawai ya tambayi lafiyarta sannan suyi sallama,
A wannan lokacinne abida tasamu sadam yanda takeso yana bata kulawa sosai fiyeda yanda yake mata lokacin suna nigeria a yanzune takejin dadin zamansu da sadam dan sam yadaina yimata halin ko inkula kamar yanda yakeyi mata abaya sannan itama halayenta dayawa tabari tadauki shawarar mummy tana bashi kulawa,
Rashin sawwama tare dasu ya sanya tagane wanene ainihin mijinta zamansu yana dadi sun fahimci juna sosai, ayanda takeson zamansu a yanzu tayi alqawarin bazata kara barin sawwama tadawo cikin rayuwarsu ba, zatayi duk yanda zatayi taraba alakar sawwama da sadam, zatabi duk wata hanya don nesanta sawwama da sadam,  ta lura cewa sadam idan yana tareda sawwama ne ya sanya bazai iya bata kulawaba ta lura zamansa da sawwama ne ya sanya baya iya ganinta dawani matsayi, farin cikin da take ciki yanzu sam bataso ya gushe tanaso ta dawwama a cikinsa shiyasa  take jin aranta duk wanda zaiyi  barazanar tarwatsa mata wannan farin cikin a yanzu to zata iya daukan mataki akansa ko wanene koda kuwa mahaifiyarsa ce, bare sawwama wacce  zata iya rufe babinta cikin rayuwarsu gabaki daya,

Kullum aikin kiran mummy takeyi akan kada taturo musu sawwama dan zamansu yana dadi acan, mummy takance kuyi zamanku ko kofa takashi bazata ba bare naturo miku ita, da dalilina ai na turaku karatu, na turakune dan kuyi nesa da ita idan naturo muku ita ai anyi ba'ayiba kenan,

Sadam kuwa yafara takurawa mummy akan zancen karatun sawwama tun mummy nayi masa yan kwana-kwana har tadawo tace wancan tace wannan, tazo tace masa admission ne ba'a samuba sadam yace bbu damuwa idan admission ne zai nema mata d kansa a school dinda suke tunda gasu a school din,
Jin haka yasanya mummy tace ai cikin sawwaman ne yayi girma dayawa kamar wanda zata haifi yan biyu shiyasa banason tamotsa ko nana dacan,
Sadam dajin haka jikinsa yayi sanyi da bazaisi abunda zai wahalarda itaba a yanayinda take a yanzu, tunda yaji mummy ta ambaci yan biyu yafara murna yana addu'a Allah yaza yan biyunne,
Mummy kuwa ta fadawa sadam ne haka amma bbu wani mugun girma da cikin sawwama yayi kamar na yan biyu yadaiyi girma bbu laifi kuma dake cikin fari yasaba wannan girman so baza'a kirashi da yan biyuba,
Sadam kuwa yanacan yanada murna ance cikin sawwama kamar yan biyu,
Haka yakira sawwama ya matsa mata saida tura masa pic din cikin yagani tadauki pic din tatura masa akaco sa'a kuwa cikin yafito yayi radau a hoton aiko nan sadam yakara rikicewa shi duk zatonsa yan biyunne,

Sa'i-sa'i sawwama sukanje gaida mummy itada halima dake a wajanta take, ba yabo ba fallasa karbarda mummy takeyi musu kennan,

Cikin sawwama yayi girma mummy nagani amma koda sau daya bata taba tunanin cewa zata sanya sawwama tadawo gidanta ba dan kada rashin lpy ko nakuda tatashi suna su biyu a gida bbu wani mai tamaka musu ko ajikinta wai injita tsunstun dayaja ruwa shi ruwa kan doka,

Da cikin yafara tsufa sai suka daina fita dinma gabaki daya koda yaushe suna gida, ko sau daya mummy bata taba neman yanda sukeba bare ta lekasu taduba lpyrsu dady idan yayi magana ya tambayi sawwama nuna masa take tana zuwa dubasu akai-akai,
Dady yace mi zamansu acanma hankalina bai kwantaba tunda ita dayarma ba babba bace kanwar tane so zamansu acan akwai dan hatsari idan kikaje kiyi musu magana sai su shirya ki ebesu su dawonan dan zamansu acan din su kadai haka ba dabara bane,
Mummy tayi saurin cewa eh toh nima nayi tunanin hakan amma kuma dear naga ciki nata dasaura ne yanzu nabari idan tashiga watan haihuwa  saina daukota tadawo nan yanda itama zaman bazai ishetaba,
Dady yace toh hakanma ai yayi ni nadauka zuwa yanzu ai tashiga watan haihuwar tata, mummy tace A'a dasaura dan yanzu zata shiga wata na takwas,
Dady yace toh Allah ya sauketa lpy dai amma da zarar yashiga na taran sai adaukota tadawo nan din shi kansa sadam din idan yasan tananan hankalinsa zaifi kwanciya da ace tana can,
Mummy tayi shiru bata sake tankawaba, dan ita bazata yarda ta daukota ahadata da dawaniya ba, tasan cewa cikin yawuce 8month da saninta tafadi hakan nufinta sai dai dady yaji haihuwar kawai, idan yaso lokacin sai tace anbata a lissafine."

Sassafe saawwama suka shirya suka tafi gidansu acam zasu wuni zuwa yamma saisu dawo,

Mama kadai suka samu baba yafita kasuwa mamanma tana shirin fita anguwa sukazo shine tafasa fitar,  bayan sun gaisa mama tana tambayan su mummy sawwama tace da gobema ko jibi nakeson zamuje mu gaisheta, da rashin fahimta mama tace ba daga can kuke ba kenan? Sawwma tace eh daga gida muke sai gobene zamuje in sha Allahu,
Mama cikin mamaki tace acan gidanki kenna kuke zaune?
Halima tace eh da ina zamu zauna mama idanba gidantana? Mama tace wannan ai rashin hankaline sawwama da wannan tsohon cikin kuke zaune ku biyu agida?
Sawwama tayi kasa da kanta halima tace to ai mama akwai mai gadi, dankwalo mama tayi mata tace ungo naki shi mai gadin mai zaiyi muku idan nakuda tatashi?
Ai dare akeji sawwama, ni dakukaga nazauna nayi shiru haka duk a tunanina kunacan gidan mahaifansa ko waya mukayi baki taba nunanin acan kuke zaune ku kadaiba, ai zamanku duka yara acan bazaiyiwu ba gaskiya kodai ki koma can gidansu ki zauna kokuma kidawo nan da zama cikin biyu dole ayi daya, amma bazan yarda ayimun wannan sakiyar da bbu ruwanba bazai yiwuba, haka mama tayita banbaminta sawwama ita dai tayi shiru kawai ta sunkuida kanta kasa,
   Haka mama tahana su sawwma tafiya tace bazasu tafiba sai baba yadawo tukunna duk abunda yace toh sai ayi,
Baba bai dawoba sai magriba yayi murnanr ganin sawwama sosai dan ya kwana biyu bai gantaba bakuma zai iya zuwa gidanta da sunan yaje ganinta ba,
Saida baba ya huta yaci abinci sannan mama ta sanar dashi halin da ake ciki,
Baba yace toh yanzu dai bazamu yanke hukunci kai tsayeba haka tunda ikonta ba a hannunmu yakeba yau zasu koma gidanta, idan sunyi waya da mijjnta saita sanar dashi halinda ake ciki saita nuna masa hatsarin zamansu haka su kadai yara a agida a wannan yanayin da take ciiki abunda yafada toh hakan za'ayi,
Mama tace amma babann sawwama ai baza'a biye musuba tunda dagashi har itam yarane abunda muka hango su bazasu hango ba zamansu can din babban hatsarine tunda haihuwa ake zance haihuwa kuma ba karamin abu bane da za'ayi wasa dashi,

Baba yace eh hakanma dolen dai sai abunda yace idan yaki tadawo din sai adauki wata daga cikin dangi babbar mata haka saita zauna musu acan din in sha Allahu, Allah zai kare zai kawo komai cikin sauki,

Baba da kansa yaraka su sawwama gida saida ya tabbatar sun shiga ciki kafinnan yajuyo yakoma gida."

Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,

Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.

Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."

✔️ote
Comment
Follow
Share plss

To be continued
Zaynab Alabura

💞

ƘADDARAR RAYUWADove le storie prendono vita. Scoprilo ora