8

557 8 0
                                    

*SHU'UMAR MASARAUTA*

       ©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga ɗaukan tsattsauran mataki don haka a kiyaye.

*Masu ƙorafe-ƙorafe ta pc da groups zan rage 100 daga yau zuwa ranar da zan gama free pages. Free pages za su ƙare a page a 10 daga yanzu zuwa ranar duk mai son karanta littafin za ta turo 400*

  SHAFI NA TAKWAS

   RIGAR ARƊO

   A gajiye tuɓus suka dawo gida sakamakon yawon kiwon da suka je cikin dokar daji, zamansu babu wuya wata farar dattijuwa ta ɗauko ƙorai guda biyu sai da ta fara zuba nono a cikinsu ta miƙa wa mai gidanta Baffajo. Ta jima a tsugunne tana jiran ya karɓa tana ɗagowa ta lura da yadda ya dulmiya cikin kogin tunani, a sanyaye ta kai hannu ta taɓa shi.

"Yanzu Baffajo ba za ka daina wannan tunanin ba? Idan kai kana yi ni kuma sai ƙaƙa?" Ajiyar zuciya ya sauke. "Inna wuro aradun Allah lamarin yaron nan ƙara ci mini tuwo a ƙwarya yake, yanzu a ce ɗan mutum ba shi da abokan rayuwa sai gidan tururuwa da dokar daji? An ya Inna wuro ba za mu kai Kamalu wurin Malamijon farar riga ba?" Inna wuro ta yi jim cike da damuwa sanna ta furta, "Eh to hakan ma wani abu ne amma ni sai na ga kamar har da sabon shiga dawa..."

"Kayya mu ba a dawa muka yi rayuwa tun daga ƙuruciya ba? Kin manta a lokacin baya tsakiyar dare nake tsintoshi a bayan rumfar can wurin shurin da ke gabas da shi." Kamalu ya ɗago fuska a haɗe don jin abin da Iyayensa suke furtawa, motsa baki yake kamar wanda zai yi magana, amma sai ya gimtse ya kawar da kai gefe. "Kamalu kai fa ba yaro ba ne a ƙalla shekarunka sun haure goma, mahaifinku girma ya kama shi ba ka ganin sauran 'yan uwanka ba haka suke ba." Kamalu ya sunkuyar da kai ƙasa ba tare da ya kalle su ba, A'iru da ke gefe ta furta.

"Kwarankwasa dubu rannan har gani na yi yana ɗibar wani abu a kan gidan tururuwa yana sha, dubi wancan zobe." A'iru ta yi maganar tana nuna hannun Kamalu mai ɗauke da wani zoben azurfa mai ɗauke da wani irin zane.

"Da bakinsa ya ce mini tsintarsa ya yi a kan shuri wai gadon Masarautarsu ne." A razane su Inna wuro suka dube shi, Baffajo ya ce. "Kamalu wa ya ba ka wannan zoben?"

"Tsintarsa na yi." Kamalu ya furta kai tsaye ba tare da ɗago ya kalle su ba. Haushi ya fara kama Baffajo don haka ya ce, "Kai Kamalu hai ka shiga taitayinka, ba ka san dawa ba ko?" Kafin Kamalu ta ya ba shi amsa daga sama suka fara jin gudun dawakai da iface-ifacen mutane, kafin su yi wani yunƙuri tuni waɗansu Dogarai da sojojin masarauta suka farmusu cikin shammata suka riƙa taɗe su suna ɗaure su da  wasu murtuka-murtukan igiyoyi a jikin manyan itatuwa. Lokaci ɗaya garin ya hautsine ban da ƙura babu abin da yake tashi, waɗanda suke da rabon tsira tuni suka shuɗa daji. Waɗanda aka riga da aka rubuta zanen ƙaddararsu kuma tuni aka damƙe su, a cikin waɗanda suka tsira har da Salele ɗan gida Baffajo. Shi kuwa Kamalu ko da ya ga abin da yake faruwa ko gezau bai yi ba, yana nan zaune wani Dogari ya isa gare shi ya fisgo shi da niyyar taɗe shi, ɗayan hannun nasa ya sa ya bigi gefen hannun Dogari, wata irin azaba ya ji tamkar an zuba masa ruwan dalma. Da kansa ya ƙarasa wurin wasu Dogarawa da ke tsaitsaye suna ɗaure ragowar mutanen da aka kama wanda ko tantama babu sun riga da sun zama bayi. Sai da aka ɗaure Baffajo da waɗansu mutane biyu sannan aka ɗaure Kamalu, a ɓangaren mata kuma tuni aka ɗaure Inna wuro da sauran mutanen da ke cikin rigar. Kafin wani lokaci rigar ta yi fayau sai kukan dabbobi da ƙananan tsuntsaye da ke tashi.

  ƘAUYEN GANGARE

   Jiki a matuƙar sanyaye suka ƙarasa cikin ƙauyen gangare hannun Mai gado ɗauke da jaririya, tun daga ƙofar gari aka fara jefa musu tambayoyin inda suka samu jaririya sabuwar haihuwa. Sai dai amsa ɗaya suke bayarwa tsintarta suka yi a cikin gona, da haka suka samu suka ƙarasa gida. Da zuwansu babu jimawa gidansu ya cika maƙil da mutane, wasu na taya su murna ya yin da wasu suka fara tsegungumi da ƙananan maganganu. Wani tunani Umaru ya yi take ya sa Mai gado ta ɗauki jaririya har ta ɗora ruwan da za ta yi mata wanka ya dakatar da ita kai tsaye suka wuce gabaɗaya wurin Mai gari. Umaru yana zuwa fadar Mai gari ya zube ya kwashi gaisuwa sannan ya gabatar da jaririyar hannunsu da mahaifiyarta ta yi mata laƙabi da Jawahir, bayan ya tsahirta ya karɓe ta daga hannun Mai gado ya miƙa wa Mai gari, sanƙira yana raɓe a gefensa. Tun da aka ɗago jaririyar Malam Malmo ya zura mata idanu ko ƙiftawa ba ya ni, wannan ya haddasa fargaba da tashin hankali a zuciyoyin Mai gado da Umaru, sakamakon sanin Malam Malmo sarai da mugun aikinsa. A sakaye Umaru ya ɗan yi gyaran murya ya furta.

SHU'UMAR MASARAUTAR CmpltWhere stories live. Discover now