02

359 30 0
                                    

❄️❄️ *DUNIYA BIYU!!*❄️❄️

©Jeedderh Lawals

Free page 2

⋆°⋆

Kiran sallar asubahi ne ya tasheta. Tayi addu'ar tashi daga barci tare da tashi ta faɗa bayi. Alwala tayi ta fita, sai a lokacin ta tashi Hajja, bayan ta tashi ta fita ta bugawa su Badi kofa sannan ta koma ɗaki ta tayar da nafila.

Masallacin dake bayan gidan ta bi jam'i. Lazumi taci gaba da yi bayan an kammala sallar har gari ya fara washewa. Hajja ta fita kicin wajen haɗa abin kari.
Ta tashi ta ɗauke kayan shimfiɗarta ta gyara ɗakin. A gurguje tayi wanka ta fito ta shafa mai. Abin shafa hoda kaɗai ta murza a fuskarta tare da zizara kwalli a idanunta. Ba ma'abociyar kwalliya bace ita, ko bayan haka makarantarsu ba'a barinsu suyi kwalliya.

Tana gama shiryawa cikin kayan makarantarta, ta ɗauki safarta fara ƙal ta sanya, ta sungumi jakar makarantarta ƴar goye. Wata tafiya da Daddyn Abuja ya taɓa yi ya sauka a gidan lokacin daya dawo, ya kai mata ita. Ba ƙaramar masifa ta sha wajen su Badi ba kuwa. Sai da Alhaji ya kira shi da kanshi, ya siyo wasu jakunkunan irin nata sak ya kawo musu sannan ta samu sukuninsu.

A kicin ta samu Hajja tana ƙoƙarin soyawa su Badi doya da ƙwai na tafiya makaranta ita da Indo. Ta gaida su suka amsa.
Indo ta miƙa mata damammen kwastad wanda aka saba damawa Alhaji kullum da safe. Da yake ta jima da zubawa, ya fara hucewa. Ta kafa shi a bakinta tana sha kamar ruwa, sai kofin ta miƙa mata.

Hajja ta kallesu a kaikaice, "watarana sai kinje kin ƙona bakinki a banza a wofi idan baki daina yiwa abinnan shan ruwa ba!".

Ta ɗan turo baki gaba, "to ai babu zafi Hajja, kuma sauri nake yi".

Sai lokacin ta ɗaga kai ta kalleta, tace "to ai bani na ƙaƙaba miki tafiya makarantar da kanki ba ko? Tun yaushe nake bin kanki akan ki dinga bin su Badi'atu kuna tafiya? Amma shegiyar kafar kai irin taki, kin ƙi, wai ke kada ki makara, sai kace ke kika kawo boko duniya!".

Ameenatu dai bata ce komi ba, sai murmushi data ɗanyi, tace, "to ni na tafi sai na dawo!".

Ta juya da sassarfarta zata tafi, Hajja tace "dakata in zuba miki ki tafi da abinci mana".

Bata yi musu ba, taja tunga ta tsaya. Da alama yau Allah Ya jiƙanta Hajja bata ce zata ba su Fauzah su tafi mata dashi ba. Kusan kullum sai dai a ba su abincinta su tafi mata dashi. Basu taɓa kai mata ba, hasalima basu taɓa kwatanta gaya mata an basu abincinta ko yadda suka yi dashi ba. Ta taɓa kai ƙorafinsu wajen Hajja, sai dai abinda ya faru bayan nan sai daya sanya tayi dana sanin ɗaga baki tayi magana. Bata manta irin cin mutuncin da Anty Mommy tayi takanas-takano ta tako kafa tun daga gidanta tazo ta sauke musu, kan cewa ita Ameenar tana bibiyar ƴaƴanta da sharri, akan abincin banza dana wofi, bayan tasan cewa sun fi ƙarfinshi.
Bata sake ɗaga baki tayi magana ba daga nan, har lokacin kuma bata sake zani ba.

Hajja na miƙa mata ƙaramar kular data zuba doyar a ciki, ta zuge jakarta ta saka a ciki. Da sauri ta musu sallama ta juya ta bi ta babban falo. Lokacin data wuce ta ƙofar ɗakinsu, ta jiyo sautin hayaniyar su Fauzah, da alamun tashinsu daga barci kenan. Ko dai tashinsu kenan, ko kuma sun koma barcin bayan sallar asubahi. Ta wuce zuwa ɗakin Alhaji.

Yana zaune akan abin sallarshi yana jan carbi. Yahya matashin yaron da yake musu share-share yana gyara mishi ɗakin. Tayi sallama ta durƙusa a gefenshi, a nutse ta gaida shi. Ya amsa cike da fara'a.
"Har an fito za'a tafi ne, mai babban suna?". Duk duniya shi kaɗai ne da marigayi mahaifinta suke kiranta da wannan sunan.

A ɗan kunyace ta gyaɗa kai, yace "to Allah Ya tsare hanya, a dawo lafiya. A kuma kula da hanya, banda biyewa abokanan banza".

Tace "to", a hankali ba tare data motsa ba.
Tunda yaga haka yasan cewa da magana, sai ya gyara zaman shi sosai. Yace "Yaya aka yi ne mai babban suna?".

DUNIYA BIYU!!! Where stories live. Discover now