04

288 22 0
                                    

❄️❄️ *DUNIYA BIYU!!*❄️❄️

©Jeedderh Lawals

Free page 4




Alhaji Badamasi da Alhaji Hamisu yan uwa ne uwa daya uba daya. Su biyu ne kacal wajen iyayensu, sun kuma taso cike da hadin kai, son juna da taimakon juna. Sun samu kulawar iyayensu dai-dai misali, sun kuma samu ilimi na zamani da na Muhammadiyya. Sun rabu da iyayensu tun a zamanin samartakarsu, sun rabu dasu cikin sanya albarkarsu da fatan alkhairinsu.
Mahaifinsu Alhaji Sama'ila ya kasance ruwa biyu, mahaifinshi ya auri wata baturiya Janet da taje karatu a jami'ar Ikko, shi kuwa lokacin yana yan sana'o'inshi a can. Bayan sunyi auren, auren ya ki ya yiwu. Sunyi auren akan sharadin zata musulunta, sai bayan auren sannan ya fahimci dalilin da yasa ta aure shi, ashe da manufa biyu ta aureshi. Tana so ta samu takardar zama a Najeriya ce ta din-din-din. A cikin halin zaman doya da manja suka haifi dansu na farko Sama'ila. Yana da watanni takwas Janet ta sake samun wani ciki, nan rigimar da basu taba yin makamanciyarta ba ta tashi. Tace zata zubar da ciki, shi kuma yace bata isa ba. Rigima fa ta safe daban, ta yamma daban. Kwana uku suna kaiwa suna kawowa akan haka, ana hudu dai sai ganinta yayi a gabanshi. Ta fada mishi taje ta zubar da cikin da yake ta tayar mata da jijiyar wuya akai, don haka ya sama mata lafiya. A take ya dauki takarda da biro, ya dankara mata saki dai-daya har uku. Washegari sai sammacin kotu ya buga mishi kofa tun da safe. Taje kotu ta fadi karya da gaskiya, wai ya rabata da iyayenta akan zai kula da ita, kuma baya kulawa da ita din.

Nan aka shiga kotu aka hau fafatawa, zamansu uku a kotun, da yake yana da shaidunshi, makotansu, akan duk irin dibar albarkar da take masa da batun zubar da ciki, alkali ya yanke hukunci. Dama bisarta ta kare, suka kadata kasar Landan. Shi kuwa ya tattara kayanshi gabadaya da dansu da tun a kotu ta fita tace ba zata rike shi ba, ya koma Katsina inda nan ne mahaifarshi. Ya samu wata bazawara ya aura. Allah bai kara basu wata haihuwar ba har ya rasu.

Gabadaya Badamasi da Hamisu haka suka dauko jinin mahaifinsu Sama'ila. Haka zaka gansu jawur dasu, ko bayan sunyi aure sun hayayyafa, yawancin ya'yansu sun dauko jininsu, hakan yasa mutane suka fara kiransu da Turawa. Ko kwatancen gida ne, ka ji an ce gidan Turawa. Har lakanin ya bi su.

Bayan rasuwar iyayensu, kowannensu ya kama sana'arshi yana yi. Shi Badamasi ya fara sana'ar sayar da kayan masarufi, Allah Ya daukaka mishi Ya sanya mishi albarka, nan da nan yayi arzikin shi yayi fice. Shi kuwa Hamisu ya kama sana'ar sayar da kayan sanyawa. Shago guda ya bude, ya zuba yadika, atamfofi, kayan sanyawa na maza da mata, shima nan da nan likkafa ta bude, ya fara zuwa kwatano yana saro kaya.

Karayar arziki ta sameshi kai tsaye, lokacin daya auri Hajara (Hajja) da shekara daya. An saro kaya himili guda daga Kwatano, suka nutse a cikin ruwa. Ba ayi hakan da cikakkun watanni biyar ba, shagonshi na kaya ya kama da wuta, ba'a fitar da komi ba. Nan fa 'yan uwa da dangi suka mishi caa, akan ya auro musu mai farar kafa, yayi kunnen uwar shegu dasu, kasancewar shi mutumin da bai cika daukar gutsuri tsoma ta mutane ba. To da yake ma dan uwanshi mai yawan taimakawa ne, yana iyaka bakin kokarinshi wajen ganin cewa ya taimaka mishi. Sai dai da yake shi din mai zuciya ne da son neman na kai, baya karba daga gareshi haka siddan.

Kusan a lokaci daya suka yi aure. Badamasi ya auri Fatima, wadda aka fi sani da Uwale, wata yar unguwar Kan Giwa. Watanni bakwai tsakani shima Hamisu din ya auri Hajara. Bayan karayar arziki ta samu Hamisu, haka Badamasi ya hada su su duka da matansu ya kaisu makka suka sauke farali.

Hajara, da tun da suka dawo daga Makkah, sunanta ya koma Hajja Hajara. Babu wanda ya isa, hatta da yan gidansu ya kirata da Hajara gatsar, bata yanka mishi magana da gorin da suka fi karfin jin shi ba, nan da nan Hajja Hajarar ma ta bata, sai Hajja kawai.
Haka take a zaune ita kadai, bata sayar da ko kullin gishiri sai Hamisu ya nemo ya bata. Idan aka yi rashin sa'a kuwa ta nemi abu a wajenshi bashi da halin yi mata, sai dai kawai ya rufe kunnuwanshi ya kuma kai zuciyarshi nesa.

DUNIYA BIYU!!! Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang