26

886 101 5
                                    

*MIJIN KANWATA..*!
_(k'addarata)_

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty❤️*

*Page 26*

Haka Rayuwar ta cigaba da Tafiyar musu cikin Kwanciyar hankali da Natsuwa,Sulaiman ya shiga Rayuwar Sunaima ya zama jinin jikinta batare data sani ba Ya riga yagama Fahimtar lagonta sai yake bi da ita ayadda take,yana kuma samun kanta aduk Lokacin Daya bukaceta.
Karfi da yaji dai ya bar ma Inna su Wasim ko tayimai mganarsu sai ya basar,sai dai su suje su dubasu ranar da ba aiki,su dawo tun yaran na Damuwa suna saka a kirasu a waya har sun fara sabawa da Chan din suma su Inna sun saba da yaran Tunda gidan ba yara sai zaman su Wasin din ya raya gidan sosai fiye da baya ko domin Gilmarwarsu da wasannin da sukeyi a tsakar gidan,Shi yaro kowa yaya yake a waje yana da Dadin zama.
Mganar zuwa kargi kuwa ta gaji ta Dainamai mgana saboda in tayimai mganar yaushe zasu je sai yace mata ta bari tayi ciki Tukunnah Daya fadi haka sai tayi shuru kunya bazai barta ta iya cemai wani abu ba,Shima yana san daya fadi haka zai kashe bakinta,Ko kuma yace mata ba yanzu zai kaita ba sai ta fara tsshi Dakyar saboda Maimartaba ya Tabbatar da Jarumtar Takwaransa Daya fadi haka zatayi Fuska bazata kara mgana ba Shi kuma haka yake so sai ya koma yana Tsokanarta yana Dariya Dukkansu batare da sun sani ba sun riga sun saba da junan da Rabuwa baza tayi musu sauki ba.
Sunaima Mijin kanwarta ya zama komai nata bata sani ba ya zama Jini da Jijiyarta Bata isa ta Dakatar dashi ba koda yana wani abun in ta fara Kiran Sunansa Saraki kamar ita ta Radamai Daya yi mata wannan Saukakkan Kallon nasa sai ta yi shuru ta koma ta lafe byan ta basa Duka Ragamar Rayuwarta gabadaya Sun zama Duniyar junansu batare data sani ba.
Wajen aiki kuwa Faufau ya hanata hawa adaidaita ya fada ya kara fada in ta sake Hawa bai sani ba ita da Allah,In Aikin safe gareta su zasu kaita su ijiyeta kafin su wuce wajen aiki,in kuma na rana ne Sani Zai baro ma"aikata yazo ya kaita in kuma aikin Dare ne Sulaiman da kansa yake kaita in bai dawo ba Sai ya Turo sani ya kaita In kuma tatashi da Safe Kafin Sani yazo Sulaiman zai je ya Daukota Daga wajen aiki Ita gani take wahalar tayimai yawa akwai tarin Hidimomi ga Kai yara makaranta Tunda Sani shi yake zuwa ya kaisu bayan ya ijiye Sulaiman a kamfani in sun tashe yaje ya Daukesu ya maida ma Inna in kuma bai samu Lokaci ba Ahmad ke Daukosa acikin adaidaita.
Ranar Sunaima tace ya kyaleta ta rika Hawa adaidaita tana Dawowa gida Saboda Zirga Zirga.
Wani kallo yayi mata na kin ma raina ni kafin ya sake maimaita mata ko bai sani ba da auransa in ta kara Hawa adaidaita ita da Allah ai sai ta kama bakinta Sulaiman ya Samu matsayi azuciyar Sunaima saboda kyakyawan Hallayarsa Ashe haka yake da Saukin kai da Dadin mu"amala sai da ta Zauna Dashi ta Fahimcesa Mutum ne bamai yawan Fushi ba Mutane na ganin kamewarsa ita kuma So nice take ganinsa Domin duk abunda zai sata Farinciki shi yake yi shidai yaga Tayi Dariya hakan shine Muradinsa sannan yana da Hangen nesa da Dadin Zama da Dattako da Daraja na gaba dashi Hallayar sulaiman masu kyau ne da bazata iya kirgasu ba.
Sai da suka samu wannan kusancin take kara karantarsa kamar yadda shima ya karanceta Shiyasa ya shiga Cikin jikinta da zuciyarta yayi babakere batare data sani ba yanzu ko Tunanin mijin kanwarta ne bata yi in ma ya tuno mata hade rai takeyi Saboda bata da tacewa ya riga yagama Sanin Rauninta gaba da baya.
Bangaran iyayansa kuwa yanzu sai Hamdala ko bata kira Hajiya ba ita da kanta take kiranta Tana tambayanta Lafiyansu data yaran ita da Hajiya karama haka kannensa ita kam sai dai Godiya ga Allah kawai.
Acikin Tsukin Hajiya tazo kargi gaida Fulani da bataji Dadi ba ita da Hajiya karama dasu Safiya Mota guda Daga kargin Kaduna suka sauka Ranar Lahadi ne tana gida ba aiki Sunaima ta rasa ina zata sakasu saboda Karramasu,Sulaiman yana gida shima Jiya sukaje kargi shi da Saifullahi suka Duba Fulani Sunaima taso zuwa sulaiman yace da sauranta Dole ta Hakura basu wani Dade ba abinci kadai sukaci sukayi Sallar La"asar Sukace zasu Leka su gaida Hajiya giwa itama tana ta fama da kafa sai Sunaima tace zataje ganin da Hajiya a wajrn yasa Sulaiman ya barta Tare sukaje gidam Hajiya jamila(Giwa) suka Dubata,Taji sauki ma sosai ta kuma ji Dadi daman Sulaiman ya taba kai Sunaima ta gaisheta.
Basu jima ba agidan don ma an zauna ana ta Hirar Laila da Hajiya Salame anan ne Sunaima take jin Labarin Ashe Hajiya Zaliha kawar Hajiya Salamen data Dawo daga Niger taji Kawar tata shuru gashi bata samun wayarta sai taje gidan Halin dataga Laila ya Girgixata duk ta jeme ta Lalace aiki gida kadai ya isheta ko Haraban Gidan Alhaji isa bai yarda ta Fito ba Lokacin da Laila ke fadamata abubuwan da suka Faru ta tsorata yadda suke fada Alhaji Isa ya dawo ya ganta a karce ta gudu saboda yayi alkawarin sai ya makata a hukuma Sabida ita ta Dauki Hajiya Salame ta kaita gidan Boka ance kwana Daya ta kara ajos ta koma agadez.
Ita kuma Hajiya Salame tana chan Shashen Bayi,Tana shan azaba da Wahala Hajiya uwa taje ganinta aboye sai Rokonta take yi ta taimaka mata ta Roki Maimartaba ya yafe mata Hajiya Uwa tace bada ita ba Dole ta Girbi abunda ta shuka gabadaya yn"uwan nata ba wanda ya Tsausaya mata gwara ma matan Akan mazan su Abba basu taba cema Maimartaba don me ya aikata haka ba Haka Fulani Tashin Hawan Jininta Duk Damuwan Salamen ne Kilishi kuwa data taba Yima Maimartaba mganar afuwa ga Salamen Sai da ya Bata mata rai Daganan bata karamai mganar ba.
Sunaima na gefe tana ji suna mganarsu batace komai ba Hajiya Tace Allah ba azzalumin kowa bane ita ta bar Salame da Allah Cutar da tayi mata..gashi nan tana ganin Sakamako..Ammh ta yafe mata Kanta tayi mawa..!
Sun dai Tattauna Cewa In Maimartaba ya Sauko matan zasu yi Hadaka suje su samu maimartaba su bashi Hakuri su gani ko za"a Dace Hajiya tace zataje Saboda Ta nuna ma Salame har Abada ita bazata iya cin Amanarta ba.
Nan gidan suka bar Sunaima Tunda Sulaiman yace zai zo ya Dauketa ashe bayan fitansu Gidansu Sunaima sukaje sai dai Inna ta gansu kamar Daga sama ba kowa agidan sai ita Kadai su Wasim Ahmad yakai su Islamiya ya wuce wajen koyon Sana"arsa.
Inna tayi musu karban ban girma sosai basu dai ci komaiba suna Sauri sun sha ruwa Sai ga Hajiya na kara Bama Inna Hakuri ita kuma tace bakomai Duk an zama Daya suna Shirin Tafiya sai ga Baba ya tsaya suka gaggaisa kafin su wuce Inna ta rasa me zata basu tana da garin kunu da Kifi Dakakke bushasshe ta Juyo musu ta bama su Safiya Hajiya nata Godiya Har Zaure suka rakasu Sun kawo ma yaran Tsaranban lemuka Katan Hudu da Kayan Kwalama Daman Hajiya tasan suna wajen Inna Tunda Sulaiman ya Fada mata.
Sunaima bata sani ba sai da Inna ta Kirata ta fada mata tayi ta mamaki ta Kira Hajiya tana musu ya suka koma Gida Ta hada da Godiya Hajiya tace Bakomai Ita take fadama ma Sulaiman Shima har acikin Ransa yaji Dadi yana fadin wani kaddaran in ta Sameka kamar wata Hanyace ta Warwarewan duka lamuran mutum Shidai Lailace kaddaransa sai gashi Sanadinta komai ya Daidaita Lalle Allah ne abun Godiya ba Mutum ba.
Ita kanta Sunaimar taji Dadi ko yaya aka je aka Duba naka sai kaji Dadi aranka sai kuma alokacin take kara Tuna Nasihun Inna datake yawan Fadamata wata rana sai Labari duk abunda kayi Hakuri zai zo ya zama Sai Tarihi gashi kuwa tanagani.
Sunaima tana son su Wasim su dawo basaboda ta saba dasu dukka  Gidan iyayenta suke ammh ita din mai son yara ne in tayima Saraki mgana sai ya basar da ita Ranar dai Suna Dakinta da Daddare bayan sun gama Farantama juna rai sun yo wanka atare.
Suna kwance akan gado suna Rumgume da juna kanta na kan Kirjinsa tace"Saraki..!
Sama sama ya amsa mata Barci ke son ya Fizgesa"Uhmm..!
Cikin Kulafuncin abun tace"Wai yaushe zamu Dauko yaran nan ne..?
Kai tsaye yace mata"Ina..?ai mun barma Inna da Baba su..!
Mamaki ya kamata ta Dago Tana kallonsa cikin mamaki tace"Bangane ba..?,are u serious..?
Cikin Halin ko in kula yace"Serious.!
Ai sai Sunaima ta Mike zaune tana Kallonsa cikin Wani yanayi tace"Ammh Shine baka Fadamin ba..?na saba da yaran nan Allah Daurewa kawai nakeyi basu kusa dani..!
Yana Daga kwancen ya kalleta ido Cikin ido kafin yace"Meyasa zan fada miki..?ya"yan ki ko nawa..!?
Ido ta Zaro kafin tace"Nima ya"yana ne Tunda ya"yan yar"uwatace..!
Bai damu da yadda tayi ba yace"Eh ammh ai ya"yan Sunaira ne da Sulaiman ba ya"yan Sunaima da Sulaiman ba..!
Sunaima taji ta Muzanta idonta ya Ciko da Hawaye Cikin Rauni tace"Ni kake ma gorin Haihuwa Saraki..?
Yana Danne Dariyansa yace"Eh in kin ji Haushi ki haifi naki..Wasim dai da Wafiiya na bar ma Inna su har Abada..In kina son yara ki yi ciki ki Haihu malama..!
Yafada yana basarwa sai Hawaye shar Cikin Muryan kuka tace"Ai Haihuwa na Allah ne shi ke bama wanda yaso..Sannan ai bani zan bama kaina Cikin ba kaga kenan Kaine baka bani Cikin ka ba..Inda ka bani zan karba Tunda kasan ni ba juya bace Uwata na Haihuwa kuma kaf Dangin mu ba juya..!
Takarishe fada Lokaci Daya tana Sakin kukan daya Tokare mata Rai shi kuma sai ya fara yar dariya yana Fadin"Au abun harda gori ne..?ai nima dai kinsan ba Talasulu bane ina Haihuwa kece dai din bansan makama ba sai an gwada an gani..!
Ya karishe fada yana Daga mata gira Banza dashi tayi ta juya baya tana matsawa Daga jikinsa da Sauri ya Damkota Lokaci daya yana Rumgumeta ta baya Cikin kunnenta yake cemata"Fushi fa ba naki bane..Tsayawa zaki yi kiyi kokari ki samu cikin ki haihu sai kin wuce gorin Saraki..!
Yafada yana Dariya Turesa take yi tana Hawaye tace"Cikin ai bani zan yi kaina ba.!
Yana Dariya yace"kwarai na Tuna..bake zaki yi ma kanki ba Sulaiman zai yi miki..!
Yafada yana Tusa kansa tsakanin Wuyanta yana Shinshina Kokarin Turesa take yi tana Fadin"Saraki leave me..!
Cikin wani salon murya yace"I can"t..so nake nayi miki ciki nagani in da gaske kike ke ba juya bace..!
Fahimtar da tayi tsokanarta yake yi yasa ta juya ta fara Dukan Kirjnssa da Hannunta duka Biyu tana Fadin"Saraki Stop it..Bana son wannan wasan naka..!
Yana Dariya yana Rike hannayenta Duka Biyu yake fadin"Ni kuma ina so..Sai yaya kenan Sunaimar Saraki..?
Bata isa ta kaucema Muradinsa ba Dole ta Biye masa suka sake Lulawa Duniyar da suka Fito kamkame take dashi tana jin yana kaida kawo a Tsakanin Cinyoyinta Da gaske yake yi Cikin zai mata Domin ya Dage sosai yake Morarta son ranta da abun yazo Riketa yayi yana Nishi sai da ya tabbatar daya jiyo mata Duka kana ya Ramkwafa kanta Cikin Sauke Numfashi yana Fadin"Insha Allahu na saka mai sunan Fulani ko maimartaba..Ko ban saka yau ba inaji ajikina na saka tun abaya..
Kunya ya bata ta noke saman kirjinsa Tana Sauke Numfashi shima kara Riketa yayi sosai domin samun natsuwa acikin Ranta taamsa da Ameen Domin har ga Allah tana son yara Yau kamsai taji itama Tana so ta Haihuwa da Sulaimam ba domin mganar da yayi mata ba sai domin Haka kurum take son ganin jinin Sulaiman Daga Jikinta tasan Halinsa in yana Kusa da ita ya dinga Tsokanarta kenan Har kuka take yi mai shi kuma ya koma yana mata Dariya Daga baya sai ya koma Lallashi Daganan kuma sai a Lula wata Duniyar.
Haka rayuwa ta cigaba da Tafiya da Dadi ba Dadi da gaske Sulaiman yake yi ya barma su Inna su Wasim Duk Sati Sani zai kai musu kayam amfaninsu na makaranta su Drinks da Indomie da kwai da su Dankali da kayan abinci da kayan kwalama Har Baba sai da yayi mganar Hidiman tayi yawa Sulaiman yace da iyayensa dasu Duka Daya ya Daukesu in har yana matsayin Dansu to su daina mgana ko Godiya in yayi wani abun Dole sukayi Shuru Sunaima bata sani sai dai Inna ta Kirata ta fadamata tace ta tayasu Godiya,bai gayamata komai Shiyasa Kimarsa ta karu acikin Idanuwanta.
Har Direban Daya Daukar ma su Wasim bata sani ba,Direba guda ya Daukarmusu ya bashi motarsa 4matic ana hidiman yaran dasu,Aikinsa kawai yakai yaran makaranta sai abunda ba"a rasa ba Dan"uwan sani ne shi ya nemosa Shiyasa Sulaiman ya aminta dashi ammh fa Shi ko Sunaima in ba sani ba,bai yarda wani yaje ya Daukota ba sai dai yaje da kansa.
sai daga baya da Taje gidan Inna ke fadamata Tunda suna zuwa duk Weekend ganin yaran ko kuma Sani yaje ya Daukosu su kwana Daya Ranar Litini daga makaranta sai gidan Inna ko zuwa sukayi sun Rika rigima kenan suna Kiran Inna da Baba Sunaina abun har mamaki yake bata Sulaiman kuwa sai Dariya yake mata yana fadin tayi Zuciya tayi Ciki ta haifi nata Yara dai sun mata Yaji su Inna suke so da Baba in ya fadi haka yana shan Harara da kananun Idanuwanta dayace masu kama da an saka kuma abuta.

*******

After 1 Month...!

Kwance taki a Dakinta Daga Dakin Sulaiman ta gudo daya shiga wanka acikin yan kwanakin nan ta kasa gane kanta kwatakwata,ita dai ajikinta Lafiyarta kalau sannan batajin wani Ciwo sai dai abu daya bata kaunar Sulaiman yace zai rabeta Koda na dan Lokaci ne yanzu zataji ranta ya baci Kafin agama kuwa har ranta takejin wani Kuna tarasa meke damunta Tun tana Daurewa baya Lura har ya Fara ganewa tana Gudunsa bai kawo komai ba yazata irin Normal din nan ne Tunda ba Laifi yana Damunta sosai Kuma yasan tana Kokari.
Yau din ma ya dawo aiki ne ita yau bataje aiki ba sai gobe zata koma Mrning,Har wani Salama ta samu Daya Fita itafa ko Kamshinsa batason ji kwata kwata Tafiso ta zauna ita Kadai wanka yace tayimai taki yimishi bai damu ba ya shiga wanka agurgije ta fitomai da kayan da zai saka ta gudo Dakinta sai dai bata Tsira ba sai gashi ya shigo Tana Daga kwancen Sai ta fara barcin karya gabanta na Faduwa Kada yace zai yi wani abu da ita.
Shi kuma harga Allah bai Fahimceta ba Gadon ya haye bayan ya Zare jallabiyan Jikinsa yana Fadin"Shine kika gudu ko..?na lura a kwanakin fa kin fara zama Raguwa ko muguntar taki ce tatashi..?
Yafada yana Rabawa ajikinta tana jinsa tayi kamar bataji ba Numfashi ta Dauke Kamshin Turaransa har hawa kanta yake yi yanzu ganin taki Motsi yasa ya fara Shafata yana dan matsa Jikinta da Saman Nonuwanta Taki ko Motsi sai abun ya bashi mamaki Tashi yayi ya kunna Wutar dakin Haske ya bayyana Abun mamaki Hawaye ya gani acikin Idanuwan Sunaima Cikin Mamakinta yace"What all dis Sunaima..!
Shuru tayi ta kasa mgana sai kuka Saboda batasan me zatacemaiba, ganin haka yasa ransa yayi zafi Cikin Karyewan Murya yace"Saboda zan kusance ki yasa kike kuka Sunaima..?Saboda zan karbi Hakkina yasa kikayi min mgana kikayi banza dani..?wato ga Dan iska naje na karata..!ko..?
Tana jin haka ta Dago tana kallonsa ta Bude zatayi mgana ya Tashi Daga kan gadon yana Fadin"Shikenan baxan matsa miki ba..Ammh ki sani In dai Hakkina ne kuma kika hanani keda Allah Sunaima!
Da sauri ta Dago Jikakkun Idanuwanta tana kallonsa kafin tace"Saraki Allah ya isa again..?
Kai tsaye ya juyo yana kallonta kafin yace"Nidai ban ce ba..Nace dai in da gayya kika hanani abunda Allah ya Hallatamin keda Allah..!
Daga haka ya wuce Tiolet yana Banko kofar sai da ta tsorata Tunda suka karbi Kaddaransu bata taba ganin Fushin Saraki haka ba sai yau kuka ta fashe dashi me zatace mai..?bataso ya Rabeta tana jin Haushi..?ai sai abun ma yafi haka ta rasa meke damunta kamar wacce akayi ma asiri ta kuma rasa wazata fadamawa ta bata shawara sai ta koma tana kuka Sosai tana jinsa ya Fito ya saka Jallabiyansa ya hau gadon ya kwanta chan gefe ya Juya mata baya bayan ya Rage hasken Dakin yau ne rana ta farko da suka Raba Jikinsu da juna wajen barci Kowa bai samu wani barcin Kirki ba ita kuka ta kwanayi shi kuma Juyi yayi kwana Tunanin wani abu yayi mata Zata Dinga gudunsa duk a iya Tunaninsa bai samu ba.
Asuba nayi ya fice bai sake bi ta kanta ba wajen aiki ma Sai da Sani ya kaisa wajen aiki kana ya Dawo ya kaita Ko gaisuwan da tayimai da Safe Dakyar ya amsa tana so ta bashi Hakuri bata samu Fuskar haka ba Dukkansu da Bacin ran juna suka tafi wajen aiki.
Karfe Biyu zata tashi aiki,Lokaci nayi ta Kira wayarsa daman haka take yi ta Fadamai sun tashi sai ya Turo mata Sani sai dai tamai kira yafi Biyar bai Dauka Shedan sai ya Zugata Ranta ya baci kan me zai mata wannan Wulakanci daman bata saka aka ba Bata Damu da mganarsa na in ta kara Hawa adaidaita bai yafe ba ta Fita bakin asibitin ta Hau adaidaita zuwa gida.
Abunda bata sani ba Sulaiman ya ganta Sanda ta hau adaidaita Suna da Meeting yau yana wajem Meeting din kuma wayarsa na Silent bai ji ba Sai da suka fito Sani ya koma gida baya jin Dadi Sulaiman yace yaje asibiti adubasa Daganan ya je gida ya Huta key din Motar na hannunsa Ganin kiranta yasan tatashi aiki ko Mgana ba basu gama da bakin nasu ba ya bar ma Saifullahi Sallahu yana sauri ya Hau Mota yaje ya Daukota kwata kwata Fushin Dayake da ita bai kai ya Wulakantata ba
Daidai yazo bakin asibitin ita kuma suka fito ita da Aneesa kowacce ta Hau adaidaitan barayinta Har Aneesa na mata tsiyan yau ina Direban Mijinta bayanan kawai tace batason wata mgana yasa tace haka.
Ran Sulaiman ya baci Sunaima bata taba bashi Haushi irin ranar ba wato Ita zata nunamai iyakarsa bari ta hau Yadade bai ce ita da Allah ba.
Saboda bacin rai ma yasa ya juya bai nuna ma ya ganta ba ya koma kamfani Ransa abace bai kirata ba Sako ya Tura mata.

"Kin fi so Allah ya kamaki akan laifin da mijinki yace keda Allah in kika kara..?

Haka kawai yace mata tana Gida alokacin dataga sakon bata Dade da Shigowa ba wanka kawai tayi magajiya ta shigo mata da abinci aranta tana mamakin waya fadamai ta hau adaidaita kamar ta Damu sai Wata zuciyar tace wayaja..?kawai sai watsar dashi Aranat har ya dawo bai nemeta ba Haka itama bata nemesa ba Kuma washegari ma bata jirasa ba ta Shirya taje ta Hau adaidaita tatafi asibitin aranta tana Fadin Allah bazai taba kamata ba Tunda Laifi na wajebsa shi kuma wannan Taurin kan nata ne ya bakanta mai rai ya Fita batunta Satin kaf basa shiga Harkan juna Kowa na Dakinsa gaisuwa kuwa sai in sun hadu Gad da gaf Sunaima ta gaishesa ya amsa adakile ko yan aikin sun Fara Fahimtar akwai matsala haka ma Saifullahi ganin gogan ya Rage walwala sai dai shima Daya tambayeshi yace bakomai.
Kwana Uku suna wannan gabar Matar Saifullahi Khadija ta Haihu aiki akayi mata asibiti.

*Janafty*

MIJIN KANWATA(K'ADDARATA)Where stories live. Discover now