(9).

0 0 0
                                    

*ƘURARREN LOKACI*

(9).
Masu iya magana sun yi gaskiya; Zuciya bata da ƙashi.
Tsautsayi ya kawo Mijinta ɗakin da nake yana roƙona na so shi shi zai iya aure na. Na dinga roƙon shi ya yi haƙuri ba zan iya yin haka ba, Daidai lokacin da yake sake mini magiya da faɗin shi har rabuwa da ita zai iya ta faɗo ɗakin. Zagi ta uwa da uba nasha da jifa na da munanan kalamai Azzaluma butulu na yi ƙoƙarin fahimtar da ita amma kishi ya rufe mata ido.

Ni ma da zuciya a ƙirjina Na kasa jurewa ina ta ƙoƙarin ganar da ita amma ta rufe ido tana surfa min zagi saboda tsabar kishi tun ina shiru ganin abun nata ba mai ƙarewa bane tana ta aibanta ni da gorika na fusata.

Na ci gaba da mayar mata da murtani munafukin yay tsit har ta kaimu ga doke-doke bai tanka ba ta nuno ni da yatsa tana zagina nima na zage ta tas ina huci. Nan take na ɗauki jakata.

Na fito tsakar gida na ɗau ɗana na haɗo da wata ƙaramar jaka da 'yan kuɗaɗena ke ciki na fita.

Zuciyata na zafi na kai babban Titi duk da ban san inda zan dosa ba amma na ji a raina na gama tako gidanta har abada. Ban wani jima tsaye ba ya biyo ni daga baya ya dinga bani haƙuri kai-tsaye ban masa wani kwana-kwana ba na ce ba zan iya komawa gidansa ba ya janyo mini bala'i yanzu kawai zan tafi mun haɗe kawai har lokacin tafiyan mu.

Ban san ina zani ba na dinga addu'a ina tafiya har na miƙa sosai.

*
Na yarda da Farouku sosai da sosai, Allah jeho mini shi duk da baya cikin yanayi mai kyau amma ya fahimce ni, na shiga motarsa Imraan na ta kuka ya wuce da ni wani gidansa da yake hutawa. Yana ta dafe kai shi yasa ban iya yin dogon zance da shi ba.

Tun da ya tafi ban sake ganin shi ba sai bayan kwana goma cir. Ban leƙa ko ƙofar gida ba na gode Allah da abinci da ruwa matsalata kaya kawai.

Ya same ni muka tattauna sosai na masa godiya.

A ranar ya mun siyayya sosai aka yi Fasifot na tafiya Tun da asuba zamu tafi Abuja gobe daga chan zamu wuce germany ɗin.

Hakan ta kasance tun da asubahi na gama shiryawa, Direba ya zo ya ɗauke mu da kaya da ni da Ɗana zuwa Abuja Ina ta addu'o'i da gode ma Allah.

*
Wani hani daga Allah baiwa ne, Ban taɓa tunani ko da a mafarki zan tsallake Sabon Layi ba. Yau ni ce ubangiji ya karrama haka a ƙasar da ubana bai taɓa zuwa ba bare uwata Allah ya jiƙan ta.

Na yi kuka kamar raina zai fita na godewa Allah Rufaida ƙanwarsa mai kirki da ita, Muna wani gida mai kamar kwatas mu huɗu ne a ciki Rufaida a ƙasa ni saman bene, sai wasu mata da mijin turawa su biyu.

Mun shiga da himukin kayan da ya sake danƙara mana kowace ta jera aka kawo mana abinci daga wani restaurant mu ka ci mu ka yi hani'an kowace ta yi wanka muka kwanta barcin gajiya.

09117440993

KURARREN LOKACIWhere stories live. Discover now