(20) Last Page.

2 1 0
                                    

*ƘURARREN LOKACI*

©KHADIJA MUHAMMAD SHITU (K_SHITU).
09117400993.

ƘARSHE.
(20).
Gaba ɗayan Rayuwata Darasi ne mai zafi ga mai kaifin ƙwaƙwalwa!
Ban tashi cikin jin daɗi da mutanen ƙwarai ba.
Na samu darussa masu yawa cikin rayuwata, Abu na farko ba zan mance da Ummah ba wacce take ɗauke da Cutar Ƙanjamau a halin yanzu!
A da na ɗau alwashin ba zan taɓa yafe mata ba sai dai a yanzu da take cikin mummunan yanayi ba zan wulaƙanta ta ba zan yafe mata domin rashin yafiya ya janyo mana matsaloli da dama; Duk wanɗanda take rayuwa da su sun guje ta da tozarci.
Bata tausaya mana ba duk da Halin jarabtar da muka shiga mai haɗari.
Gashi yanzu tana Nadama a Ƙurarren Lokaci da ba zata yi mata rana ba bata nemi yafiya dubban Jama'ar da ta zalunta ba musamman Imaan.
Duk girman laifin da muka aikata mata bamu chancanci ta Goranta mana ba da cutar da ƙaddara ta mana kutsen ta, Ta baiwa sauran al'umman da ke zagaye da mu ƙofar zaluntar mu Yanzu gashi ita ma Tana ɗauke da ita.

Ban saki kuɗaɗe ba domin kula da ita ina bada abin da naga zan iya saboda ina fata wannan ya zama darasi ga 'yan baya.

Ba zan ɓoye ba muna zuba soyayya da Alhaji farouku sosai da sosai mai tsafta tare da Ɗanmu guda Umaar. Mahaifiyarsa ta karɓi Addinin musulunci sunanta ya dawo Aminatun.

Babu wata matsala sai dai yau da gobe.
Duk waɗanda suka karrama ni na saka masu da akhairi ni ma, Na taimaki Dr Jabir bakin iyawata da ma wasu mutanen. Ina da Wata Gidauniya shahararriya ta kare Haƙƙin mata da Yaƙi da Shaye-shaye.

Alhamdulillahi na samu ɗaukaka da nasarar rayuwa mun riƙe addu'o'i da taimkon na ƙasa da mu.

Lokauta masu yawa ina tuna kalan wahalar da muka sha. A yanzu ni Khadija Imaan, Ilhaam ce da dangi, Wanda kuma nake kan bincika dangin Abbahna.

Duk da wadatar da muke da ita ban chanja zuciyata ba da son ƙyale-ƙyalen Duniya.
Ba lallai ba ne mutum ya iya cire son Ƙyale-ƙyalen rayuwa a zuciyarsa ba domin kowane ɗan adam na burin Jin daɗin duniya.

Bakina bai huta ba saida Alhajina ya biya mana Umrah ni da shi da kuma Yara.

        *ƘARSHEN LITTAFIN ƘURARREN LOKACI.*

Alhamdulillahil Lazi bi ni'imatihi tatimmus salihat.

Ma sha Allah! Ubangiji da nashi ikon ya bani dama na kammala wannan littafin nawa.
Abin da na rubuta daidai na ƙoƙarin faɗakarwa Allah ka bani lada kuskurena Allah ya yafe mini nima Mutum ce ajiza. Waɗanda na ɓata wa su yafe mini.

Duk wacce ta karanta ta yi mini addu'a ina ƙaunar masoyana saboda Allah🥺♥️.

Ayi Following Accounts ɗina
Arewabooks
Wattpad.

#ƘURARREN LOKACI
#KHADIJA MUHAMMAD SHITU
REAL K_SHITU
#7th- friday, June - 1:AM.

www.kshitu@gmail.com
#09117440993.

KURARREN LOKACIWhere stories live. Discover now