Chapter 11-12

42 4 0
                                    

༺༻🌹༺༻
     *🇿​UℬAℛ*
  *🇭​AWAYE𝒩A*
              ֍
༺༻🌹༺༻        
     , . - . - , _ ,   "  ;
    ) ' - . .> ' '(
   /   🌹🌹    '\    
   |  🌹  🌹🌹  |
    \     🌹  /    /
        '=(\ /.='
          '-;'.-'
            ')|     ,
              || _🍃. -'
           ,_|| \_,/

*Տᴛ⌾ℛℽ & 𝒲ℛⅈᴛᴛℰℕ*
            *ɮ̋ʏ̋✍*
෴ℛαвⅈ́'α𝙩 ѕвѕ෴
         ❨ცıɠ ɠᵃ̨ι❩

*©®-Aɴᴀ ᴛᴀʀᴇ Wʀɪᴛᴇʀs Assᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ ✍🏻*
▬▬▬▬▬▬▬▬▬▬▬
➛➛➛➛➛➛➛➛➛➛➛
(wє ѧяє ṭһє ɞєśṭ ѧṃȏṅɢ ѧʟʟ wяıṭєяś)📚
https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/
Jσเɳ ɱε σɳ ωαƭƭρα∂:@Bเɠ-ɠαℓ

*_Fadila αlῖϒῠ ϻῠsα (ϻϒ δῖlαlα)❤️ kϵ δῖͷ tα ϻῠsαϻϻαͷͼϵ gαrϵͷῖ._*

𝙳𝚘𝚖𝚒𝚗 𝚜𝚊𝚖𝚞𝚗 𝚕𝚒𝚝𝚝𝚊𝚝𝚝𝚊𝚏𝚊𝚒 𝚖𝚊𝚜𝚞 𝚔'𝚊𝚢𝚊𝚝𝚊𝚛𝚠𝚊 𝚐𝚊𝚖𝚒 𝚍𝚊 𝚗𝚒𝚜𝚑𝚊𝚍𝚊𝚗𝚝𝚊𝚛𝚠𝚊 𝚑𝚊𝚛 𝚖𝚊 𝚍𝚊 𝚏𝚊𝚍𝚊𝚔𝚊𝚛𝚠𝚊 𝚜𝚊𝚒 𝚔𝚞 𝚐𝚊𝚛𝚣𝚊𝚢𝚊 *DUNIYAR LITTAFAN HAUSA TV* 𝚍𝚊 𝚔𝚎 *𝚈𝚘𝚞 𝚃𝚞𝚋𝚎* 𝚍𝚘𝚖𝚒𝚗 𝚜𝚑𝚒𝚐𝚊 𝚔𝚊𝚒 𝚝𝚜𝚊𝚢𝚎 𝚜𝚊𝚒 𝚔𝚞 𝚍𝚊𝚗𝚗𝚊 𝚋𝚕𝚞𝚎 𝚍'𝚒𝚗 𝚛𝚞𝚋𝚞𝚝𝚞𝚗 𝚗𝚊𝚗 𝚍𝚊 𝚔𝚎 𝚔'𝚊𝚜𝚊 𝚔𝚊𝚗𝚊 𝚔𝚞 𝚍𝚊𝚗𝚗𝚊 𝚔'𝚊𝚛𝚊𝚛𝚛𝚊𝚠𝚊.
https://www.youtube.com/channel/UCcAjVQ74qod9_dL0e_AqkiQ

*🌹🇵​ᴀɢᴇ ☞11➪12*

    Sosai gabanta 𝚢a yanke ya fad'i jikinta ya yi sanyi, tsoro ya cika mata zuciya, dan ta riga da ta tabbatarwa zuciyarta cewa ya gama fahimtar komai game da ita kamar ma ya juma a tsaye a wajen, duk da haka ta dake zuciyarta ba tare da ta nuna alamar komai ba, binsa da kallo ta yi, sosai ta tsira masa ido kamar yadda shi ma yake bin ta da kallon.
       Fuskarsa babu alamar walwala bare ta bawa zuciyarta tabbacin bai fahimci komai daga gareta ba.
       Wannan yasa itan ma bata d'auke kallonta daga gareshi ba sai ma had'e rai da ta yi ta k'ara d'aure fuska, duk da irin tsoron da ke cikin zuciyarta na gudun abinda zai je ya zo hakan bai sa ta saki fuskarta ba, ta ci gaba da zuba masa na mujiya.
     Ganin irin kallo da yake mata wanda bata fahimci inda ya dosa ba yasa ta yi saurin yi masa magana "lafiya ko ka zo nan d'in ne ka kuma yi min abinda ka yi min d'azu?"
      Mik'a hannunsa ya yi duk da tazarar da ke tsakanin inda yake tsaye da inda take zaune ba zai yu ta mik'o abinda yake son karb'a ba amma a haka ya mik'a hannun nasa yana yi mata magana "mik'o min wayar" a fusace ya yi maganar cikin b'acin rai.
      Gabanta ya k'ara fad'uwa a ranta ta kuma cewa shikkenan kashina ya bushe a wajen wannan mara mutuncin, kenan ya fahimci komai, toh yanzu ya zan yi? idan kuma ya duba chat d'in da mukai da Dr.Haneef ya zan yi? gashi wayar ba security.
      Cikin tsananin masifa ya daka mata tsawa wanda har sai da ta razana, maganar da ya yi shi ya katse mata guntun tunanin da take akansa da kuma tambaoyin da takewa zuciyarta wanda ko ita kanta ba tada amsar su, magana yake ta mik'o masa wayar.
      Duk da irin zafin da yake nuna mata bai sa ta ji tsoronsa ko ta matsa daga inda take zaune ba, balle ta mik'a masa wayar, sai ma k'ara dakewa da tayi ta ci gaba da kallonsa cikin d'acin rai ta fara yin magana "ban gane na mik'o maka  wayar ba, waya dai na ga tawa ce kuma ba kai ka siya min ba 'yan uwana su suka siya min banga dalilin da zaisa na baka waya ba, toh ma in na baka me za ka yi da ita?"
       Duk da irin zafin da yake nuna mata sai kuma ya gagara bata amsar maganarta sai da ya d'an yi shuru na 'yan wasu dak'ik'u kafin ya ce "eh na ji gwara da ba ni na siya miki wayar ba tunda ga shi ta dalilin danna wayar har kina iya kasa girkawa mijinki abincin da zai ci, abinda ake fad'a akan wasu matan kema ga shi ya bayyana akan ki, matan da suke k'ona girki ko kuma su manta da yin girki saboda tsananin danna waya, wannan shirmen banza ne kin je kin dafawa mutane Taliyar yara mtssww... tun da nake da ke kin tab'a ganin na ci ta a matsayin abinci?"
       Dariya ta yi kad'an a ranta ta ce aikin banza ashe ma bai gane ba Allah na gode maka da bai gano komai ba, ta kuma mayar masa da maganar da ya yi "Hmm kana tunanin kai na dafawa? idan ma kana tunanin hakan ne toh ka daina, domin kuwa ba kai na yiwa ba, ka sani ba wai sadaka aka kawo maka ni ba, ina da gidan uba kamar yadda kake tak'ama da naka ba zai yu ka runk'a takuran akan abinda ba zayyu ba".

              𑁍𑁍𑁍𑁍𑁍

    Alh. Aliyu shi ne mahaifin Haseena mutum ne na gari wanda yake zaune da mutane lafiya, a duk fad'in unguwarsu kowa ya shaida hakan.
    Alh. Aliyu na zaune a garin kano cikin unguwar Sharad'a, kuma haifaffen garin kano ne a unguwar Rijiyar  Zaki.
      Alh.Aliyu na d'aya daga cikin 'yan siyasar da su ka yi shuhra su ka kuma yi tashe a shekaru goma sha biyu da su ka wuce inda daga bisani kuma ya bar harkar siyasa al'amuransa suka ja baya rayuwa ta juya masa baya, ya zamana tamkar bai tab'a yin wata aba siyasa ba, domin komai ya k'are masa face gidan da yake ciki da sauran wasu 'yan  kadarori daya b'oye na filaye da iya na rufin asiri tun da kuwa bai rasa ci da sha ba bare kuma sutura.
      A duk lokacin da ya buk'aci siyen wani abu wanda bai fi k'arfinsa ba, babu shakka yana iyawa, ya fara yin kasuwancinsa ne tun bayan da ya bar harkar siyasa tun kafin girma ya zo masa.
     Alh. Aliyu yana da shekaru  Sittin da biyar ya d'ora d'ansa Imran akan harkar kasuwanci duk da cewa ana fad'uwa ana samun kuma riba a haka ake lallab'awa dan neman na rufin asiri.
       Yana da mata guda d'aya mai suna Haj.Asiya, yana da yara guda goma, dukkaninsu mata maza guda biyu.
     Imran shi ne babba daga shi sai Madina sannan Nabiha, sai Nasira da Jamila, Jalila da Nabila, Haseena ita take binta sannan Radeeya, da Fahat, ga duk wanda ya gansu ya san 'yan gida d'aya ne domin kuwa kamanninsu d'aya, kuma kyahunsu d'aya, kuma kowannensu yana da aikin yinsa wannan yasa suke k'ara rufawa kansu asiri ba tare da sun je nema wajen kowa ba.
    Alh.Aliyu a duk 'yan uwansa ba wanda yake zuwa wajensa sai 'yan tsirari masu zuwan ma neman ya taimaka musu su ke.
       A gidan su shi ne na uku sauran yayyensa sun rasu sai k'anne da yake da su guda uku, mata biyu namiji d'aya wato Zainab, Fatima da Alh.Maina, dukkanin su ba wai iyayensu d'aya ba, Alh.Maina mahaifiyarsa daban, uba kad'ai suka had'a, iyayensu sun juma da rasuwa tsahon lokaci.
       Haka ya ci gaba da rayuwa duk da wasu cikin yaransa sun yi aure kasancewar mata ne, wanda su ka rage ba aiwa aure ba Radeeya da Fahat ne kawai suna ci gaba da karatunsu.
     Sai dai wani hanzari ba gudu ba da yawan yaran nasa zuciyarsu ta son abin duniya ce, sun fi karkata zuk'atansu akai, shiyasa ma ko mahaifiyarsu bata tab'a barin wani yaro ya zo wajen d'iyar ta, ba tare da an shaida mata irin arzik'in da yake da shi ba.
     Abinda mai karatu bai sani ba game da Alh.Aliyu shi ne lokacin da yake ganiyar dukiyarsa cikin daular siyasa bai damu da kowa na jikinsa ba wato 'yan uwansa bare kuma ya taimaka musu, sai mutanen gari da zai yi wa su yaba asan ya yi, wannan yasa kowa ya ja jiki da shi a lokacin da ya rasa......✍🏻

*_YAWAN COMMENT YAWAN TYPING_*





🌹☞ℬıɠ ɠᗅ̨ι *¢ɛ✍🏻* *_2021_*

ZUBAR HAWAYENAWhere stories live. Discover now