17-18 Har abada

21 4 0
                                    

*HAFSATUL-KIRAM*

  ©Mai Ƙosai

Babi Na 17-18

'Ni ce ajalinka' Na tuna wasu kalamai nata, a game da baba.
     Tana fita daga ɗakin, na miƙa hannu tare da janye kwanon abincin daga gabansa. Tare da furta,
     "A'a baba, ba zan bari ba, sam ba za ka ci abincin nan ba"
    Baba ya kalle ni, cike da neman ƙarin bayani game da abin da na yi furucinsa a kai, kana ya ce,
     "Saboda me Hafsana?"
Na sake janyo kwanon ina mai ɗora shi saman cinyata tare da furta,
     "Saboda ta ce ita ce ajalinka. Baba ni kwata-kwata ban gamsu da abincin nan ba, sam hankalina bai kwanta da shi ba."
     Baba ya murmusa, gami da gyara zamansa har da tanƙwashe 'yan ƙafafuwansa kana ya ce,
     "Har abada Hafsana! Ki sani babu wanda ya isa ya ɗauki ran bawa sai dai Allah, wanda shi kaɗai ke kashewa da rayawa. Idan har kika ga na mutu to ajalina ne ya yi."
       Na numfasa ina mai sake ƙanƙame abincin cikin jikina tamkar zan mayar da shi cikina. Hawaye ya soma silalowa daga cikin kurmin idanuwana zuwa saman kumatuna, na soma girgiza masa kai.  
     'To ke Hafsa ba ta baki abincin nan kin ci ba wai? Idan har da guba a ciki to ai ke ce ta farko da za ki fara margayawa(mutuwa) kafin baba.'  Na ji wani sashi na zuciyata yana ankarar da ni haka.
    'Idan kuma ba ta saka miki ciki ba, saboda daman ai ba ta ce za ta kawar da ke ba baba ta ce? Kada ki kuskura ki ba shi abincin nan domin zai iya zama ajalinsa!' Wani bigire ya ankatar da ni haka.

      Na miƙe tsaye zumbur! Tamkar wacca aka tsikara, hannuna ɗauke da kwanon na shiga girgiza wa baba kai.
    Baba ya miƙe ya kamo hannuna, ya zaunar da ni a inda na tashi.
     "A'a Hafsana! Zan ci abincin, kuma kisa a ranki babu abin da zai sami babanki da izinin Ubangiji"
     Ya janye kwanon da na garƙame jikina da ƙyar, sai ka ce mayen ƙarfen da ya shekara jikina. Ya buɗe murfin kwanon ya zura hannunsa ciki tare da ɗeɓo lomar abincin ya kai bakinsa tare da ambaton sunan Ubangiji.
   Ganin haka ya ba ni damar zurma hannuna cikin kwanon da sauri, tare da kwaso lomar abincin na kai bakina tare da bisimilla. A zuciyata ina jin cewar mu yi mutuwar kasko.
     "Ni dai koma mene ne mu yi mutuwar tare baba." Na ce cikin wata iriyar murya wacca muryar har rawa take yi tamkar ana buga mandiri.
    Baba bai ce mini komai ba, har sai da muka kammala cin abincin kana ya dube ni cike da zallar soyayya ya ce mini,
   "Ki na tsoron na mutu ne Hafsana ko?"
    Na yi saurin ɗaga masa kaina, domin ba shi amsar tambayar da ya mini.
    Ya jingina jikinsa da bango, yana ɗan ɗaga kansa sama kamar mai nazarin wani abun kafin daga bisa ni ya ce,
    "Tabbas zan mutu, ko ba daɗe ko ba jima, sai na mutu. Ki sani cewa mutuwa tana kan kowane bawa matsawar yana numfasawa. Ubangiji da kansa ya ke faɗa mana cewar, 'kowace rai sai ta ɗanɗani zaƙin mutuwa.' Kin ga kuwa ke nan kowane ɗan adam sai ya mutu.
     Hafsana ki ɗauka idan na mutu kika wayi gari babu ni, to ajalina ne ya riske ni ba wai kashe ni aka yi ba, ki yi sani ya ke 'yata kowane abu da na sa lokacin, kamar: Mutuwa, aure, haihuwa duka suna da lokacinsu kuma idan lokacin ya yi tabbas ba makawa sai sun tabbata."
     "Ni dai ina matuƙar jin tsoro baba" Na ce masa.
   Bai ba ni amsa ba, sai ma miƙewa da ya yi yana mai faɗin,
     "Je ki yi alwala, magriba ta kawo kai."
      Ya sa kai yana mai ficewa daga ɗakin.
     Na ɗauke kwanon abincin da muka ci, jikina duk babu laka na shige madafa(kicin) na ajjiye shi, na dawo ina mai wanke hannu tare da ɗaura alwala kamar yadda baba ya umarce ni da yin haka.
     Ina cikin wanke ƙafafuwana Inna ta fito daga ɗakinta, tana mai miƙa alamar barci ta tashi daga shi. Ido huɗu muka yi da ita, ni dai na yi saurin yin ƙasa da kaina ita kuma ta wuce kicin.
    Na miƙe bayan na idar da alwalar na koma ɗakin baba na tayar da sallah kasancewar an soma kiran sallah a masallaci.
    Baba bai dawo ba, sai da aka yi sallar isha sannan ya shigo, lokacin har barci ya fara surata.
    Shigowarsa ta sanya shi tashina, na gyara shimfiɗata can nesa da shi na kwanta, ina ta saƙe-saƙe kafin bacci ya yi awon gaba da ni.

HAFSATUL-KIRAMWhere stories live. Discover now