Page Four

906 56 1
                                    

💔💔KAR KA GUJENI💔💔
(Soyayya, Yaudara, Cin Amana, Hallaci)

Ummu Subay'a

Wattpad : Ummu Subaya

🌈KAINUWA WRITERS ASSOCITION🤝🏻

Allahumma A'ixxal Islama wal Muslim

Wa Adilsh Shirka wall Mushrikin

Wa dammi Ada'aka Ada'ana Ada'addin

Wansur Ibadakal muwaidin

Bi Rahmatika ya Arhamar Rahimin

Ya Allah ka kare yan uwanmu musulman Jos

Ya Allah ka ku6utar dasu daga karafai makiyanka

Ya Allah ka sanyaya xukatansu ka basu kwarin gwiwa da tunawa da kai kadaine xaka karesu

Ya Allah ka kawo karshen fitinar nan

Ya Allah ka kawo xaman lfy da kwanciyar hankali  mai dorewa

'Yan uwana musulman Jos
(Fasbir Sabaran Jameela Innallaha Ma'a kum)

I dedicated dis page to SADNAF

Kiyi yadda kikeso dashi nakine ke daya

Ina taya Sadnaf murnan fara sabon novel dinta Kukan Kurciya

Daga jin sunan akwai darasi ssai dayake kunshe a ciki

Allah yasa ta fara a sa'a kuma ta gama a sa'a

Allah ya kara basira, daukaka, fikrah da kuma sawon rai mai albarka da amfani

Up Up Up Up

SadNaf ❤

Comments dinku na  rikirkitani
na fasamin kai bbu jini
Ina yinku irin Totally

Rally Garba
Mrs Splendid
Mom of 12
Meerna Parrot
Meela Adeel

Heart U ❤
 
                0⃣4⃣

             TUSHEN LABARI

Alhaji Bukar dan kasuwa ne mai arxiki daidai gwargwado, dan asalin Maiduguri ne kasuwancine ya kawoshi garin kano har yayi aure, ya auri Aisha cikekkiyar bahaushiya, Sam danginsa basuso auren da yayi a Kano ba sunfi bidar yaje ya auri diyar dangi, hakan yasa Sam basason Aisha suka kuma yanke xumuncin dake tsakaninsu da dan uwansu

Allah ya albarkacesu da yara biyu
Fateema ce diyar fari wadda suke kira da Zuhra don sunan mahaifiyar Aisha taci sai kuma Zulfa

Karankaf anguwarsu bbu wadda yakai Alhaji Bukar arxiki

Gida biyune ke tsakanin gidan Alhaji Bukar da Malam Iro Mai goro, shida matarsa duk 'yan asalin Kano ne, suma yaransu biyu
Aina'u da Maryam

Idan xa'a kirga talakawar anguwar Mallam Iro Mai goro na sahun farko, matarsa Asabe macece mai son abun dunia kullum ta xauna korafin talaucin Mallam Iro take, shi kuma Allah ya axurtashi da wadatar xuci

Mallam Dawooda shine babban malamin anguwar kuma Limamin babban masallacin anguwar, asalinsa fulanin Gombene malumta ta kawosa Kano, matarsa daya Goggo yaransu shida
Buba
Mammadu
Hamidu
Shatu
Ameena
Taheer

Mallam Dawooda mutum ne mai mutunci da kuma karamci shida matarsa halinsu daya, ssai ya dage akan karatun yaransa ta Arabic don yaki boko sam, Shatu na kai shekara sha uku ya aurar da ita ga dan uwansu a gombe hakama Ameena

Buba ma yana kaiwa shekara sha takwas ya auro mishi Uwani daga Gombe, bayan auren Bubane cutar ajali ta kama Mallam Dawooda, inda ya barwa Buba amanar kannensa

Karka GujeniWhere stories live. Discover now