HUKUNCIN SAKIN MAI HAILA

45 2 0
                                    

2. HUKUNCIN SAKIN MAI HAILA
Tambaya:
Malam mun samu rikici da matata ko ya halatta na sake tana
haila?
Amsa:
Ya haramta a saki mace lokacin da take haila, saboda fadin
Allah "Ya kai Annabi idan za ku saki mata, to ku sake su a
farkon iddarsu) Suratu Addalak aya ta farko, wato a farkon
tsarkin da ba ku take su a cikin sa ba. Ana nufin a halin da za
su fuskanci idda sananniya, wannan kuwa ba ya faruwa sai
idan ya sake ta tana da ciki ko tana cikin tsarkin da bai take
ta ba, domin idan ya sake ta a cikin haila to ba ta fuskanci
idda ba, saboda hailar da ya sake ta a ciki ba za’a kirga da
ita ba, haka kuma idan ya sake ta tana da tsarki bayan ya
sadu da ita, domin bai sani ba shin ta dauki ciki ta yadda
iddarta za ta zama irin ta mai ciki ko kuma ba ta dauka ba ta
yadda za ta yi idda da haila, saboda rashin tabbacin haka sai
sakin ya haramta. Ya tabbata a cikin Bukhari da Muslim cewa
: Ibn umar ya saki matarsa tana haila, sai Umar ya bawa
Annabi s.a.w. labari, sai Annabi s.a.w. ya yi fushi, sai ya ce
"ka umarce shi ya mayar da ita sannan ya rike ta har ta yi
tsarki sannan ta yi haila, sannan ta yi tsarki, sannan in ya so
ya rike ta ko kuma ya sake ta kafin ya sadu da ita, wannan
ita ce iddar da Allah ya umarta a saki mata a ita" ana togace
gurare guda hudu wadanda sakin mace mai haila yake
hallata :
A. idan sakin ya kasance kafin ya kadaita da ita ko kafin ya
sadu da ita, to anan ya halatta ya sake ta tana haila, saboda
anan bata da idda, sakinta ba zai zama ya sabawa fadin
Allah madaukaki (Ku sake su a farkon iddarsu) ba.
B. idan ta yi hailar ne tana da ciki
C. idan ya sake ta ne bayan ta fanshi kanta, (KUL'I) to anan
babu laifi ya sake ta tana haila
D. Idan ya yiwa matarsa I'laa'i kuma aka yi watanni hudu bai
dawo ba.
Allah ne mafi sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
21/2/2013

FATAWOYIN DR.JAMILU ZAREWA NA MUSULUNCI.Where stories live. Discover now