HUKUNCIN WANDA YA AURI MACE SABODA KYANTA??

12 1 0
                                    

5. HUKUNCIN WANDA YA AURI MACE SABODA
KYANTA??
Tambaya:
Malam: Akwai wani hadisi da yake Magana kan cewa kowa
ya auri mace kawai dan kyanta Allah zai hana masa jindadin
kyan, ko dan kudinta Allah zai hana masa jin dadin kudin,.
shin hadisin akwai shi kuma ya inganta?
Amsa:
Ga yadda hadisin ya ke : DUK WANDA YA AURI MACE
SABODA KUDINTA, ALLAH ZAI KARA MASA TALAUCI, DUK
WANDA YA AURI MACE SABODA KYAWUNTA ALLAH ZAI KARA
MASA MUNI Saidai a cikin hadisin akwai Abdussalam bn
Abdulkuddus wanda yake rawaito hadisan karya, don haka
hadisin bai inganta ba, kuma ba za'a kafa hujja da shi ba.
Allah ne mafi sani.
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
26/1/2014

FATAWOYIN DR.JAMILU ZAREWA NA MUSULUNCI.Where stories live. Discover now