PAGE 1

1.3K 34 3
                                    

YARIMA SUHAIL.👑*

  _STORY,WRITTEN &EDITED BY._
         *SIS NERJA'AT.*

        _COMPILATION BY._
  *HAWWA M.U (®EAL $MASHER).*
?👑👑

   _*YARIMA SUHAIL*_
        
             👑👑👑

_*Written By~Sis Nerja'art*_

_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_

_Jinjina agareki my hafnan ina tayaki murnar fara new novel d'inki *HIBBATULLAH* akowane lokaci kina a ❤👈🏻 d'ina_

_~Sak'on gaisuwata agareki my blood sis *Aufana* sonki a cikin jinin jikina yake😘😘~_

*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
      *[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE  PEN OF LOVE  😘 HEART  TORCHING  ❤  TEARS  OF  SORROWS   😭  CURDLES  🙂  GIGGLES  😁  AND  MARRIEGE  THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔

_Wannan page d'in nakine Sainah Ummun Meenal uwa tagari Allah yabar mana ke😍_

page 1⃣

garin gazban garine mai albarka da yawan mutane yana d'aya daga cikin garuruwan da ake alfahari da su.

sun kasance suna da babbar Masarautar da babu kamarta wajen girma da kyau  sarkin garin ya kasance sarki mai adalci duk kud'in mutum bai isa yazalunci nak'asa da shi ba indai har yazalunta labari yazo ma sarki toh sai yad'auki mataki,

sarki umar yana son talakawansa sosai suma suna sonsa abun mamaki wannan sarki ya manyanta domin zai kai shekaru 76 ammah indai ba ka saniba sai kad'auka d'an shekara 50 ne,  domin babu alamun tsufa a tare da shi idan dukiyarce ya tara,  idan sarautarce yana d'aya daga cikin manyan sarakuna kai intabbatar muku wannan babbar Masarautar ko da me kazo anfika.

Sarki faruk matarsa d'aya dattijuwa dada,  saidai abun mamakin duk mulkin nasa ammah 'ya'yansa biyu dukansu maza ne Ahmad shine babba sai k'anensa Abbas sun taso atare sun kasance suna son junansu.

saidai a tsarin mulkin garin indai sarki yahaura shekaru arba'in (40) saman karagar mulki toh d'ansa ba zai ta6a gadon mulkinba saidai babban jikan gidan, saidai idan babu jika namiji shine d'an sarkin yake hawa mulkin

lokacin da 'ya'yansa suka tasa yaza6a musu mata inda Ahmad ya auri d'iyar sarkin agadaz wato sultana Bilkisu,  shi kuma Abbas sarki ya aura masa  d'iyar d'an uwansa da yamutu yabari wato Sultana Sadiya.

A cikin babbar Masarautar kowa aka fitar masa da 6angarensa.

Suna zaune lafiya da matansu,  inda sultana Bilkisu takasance macece mai hak'uri da tawakkali ga ta macece mai kyauta ta kasance mai son jama'a,

inda Sultana Sadiya takasance akasin haka domin bata son talakkawa suna ra6arta dan ma mijinta a tsaye yake sun d'auko hali irin na mahaifinsu, ammah duk da haka taci alwashin ita take da burin tafara haihuwar d'a namiji.

saidai kash sultana Bilkisu ita tafara samun ciki, hankalin sultana Sadiya ya tashi sosai ganin ita ko 6atan wata bata ta6a yiba,

Bayan wata goma sultana bilkisu tahaifi d'iyarta mace murna wajen iyayen ba'a magana hatta ita kanta sultana Sadiya tayi murna ganin ba namiji bane ta haifa.

ranar suna anyi shagali sosai kud'i sunyi kuka tsakanin masarautar gazban da masarautar agadaz anzuba naira sosai a inda yarinya taci sunan dada wato Asma'u ammah ana kiranta da husna.

Bayan shekara ukku Sultana bilkisu tak'ara haihuwa inda tasamu d'anta namiji kyakkyawa domin ita yabiyo kamar antsaga kara murna wajen su sarki ba'a magana hatta su kansu jama'a sun shaida wannan haihuwar domin sarki sadaka yadinga yi da dukiya sosai, 

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now