PAGE 3

387 11 0
                                    

bayan ta gama d'auko alkyabbarta tayi tasaka sannan suka jera ita da yarima suka fito, a k'asa suke tafiya a jere, kuyangin gimbiya suka take musu baya ahaka har suka isa fada nan mutane suka dinga kwasar gaisuwa,  d'aga musu hannu kawai yarima yakeyi har suka isa gaban maimartaba dasauri dogarawa sukazo suka kare su yarima daga ganin mutane suna cewa Allah yataimaki yarima da gimbiya  azauna lafiya, har saida suka tabbatar da yarima da gimbiya sun zauna sannan suka matsa nan su yarima suka kwashi gaisuwa wajen sarki nan fadawa suka d'auka,  sarki ya amsa muku yarima da gimbiya, sarki yana godia yarima mai jiran gado ku ma angaisheku.


sannan yarima yatashi yaje kujerar da take kusa da sarki yazauna,  ita dai gimbiya tana tsugunne a k'asa sai yatsina take tana kallon mutane a wulak'ance.

maimartaba ne yad'auko wata alkyabba maikyau da tsada yamik'a ma gimbiya sumayya hannu biyu gimbiya tasa takar6a tare da yin godia sannan tamik'a ma jakkadiya,  jakkadiya tazube gaban sarki tace ranka yadad'e gimbiya tana k'ara godia Allah yaja da ran sarki mai adalci sarkin sarakai,

gyad'a kai sarki yayi nan fadawa gaba d'ayansu suka d'auka angaisheki gimbiya sarki ya ji godiar ki.

nan sarki yayi musu nasiha tare da yi musu addu'an zaman lafiya, sannan suka k'ara kwasar gaisuwa suka tashi suka fito,  cikin gida suka shiga turakar dada,

nan suka gaisheta itama tayi ma gimbiya kyauta sannan suka wuce 6angaren ummi suka gaisheta itama kyauta tayi ma gimbiya sannan daganan sukaje 6angaren umman sumayya suka gaisa daga nan suka koma 6angarensu

suna shiga yarima yanufi hanyar zuwa 6angarensa ganin gimbiya tana niyar binsa yasa yadakata da tafiyar batare da ya kalletaba yace zaki iya tafiya 6angarenki domin yanzu inason inhuta bai jira jin abinda zata ce ba yawuce part d'insa.

Gimbiya sumayya tsaye tayi takaici duk ya cikata ganin yadda yarima yadizgata gaban bayinta,  tsawa tadaka musu tace suwuce subata waje dasauri duk suka bar wajen,

nan gimbiya tanufi part d'inta cike da jin haushi.



haka sukayi sati d'aya suna shan amarcinsu tun yarima bai kulata daga baya sumayya saida tasan yadda tayi yarima suhail yad'an sake mata, ammah idan yana jin 'yan miskilancin ko sarautar takad'a masa toh ko kallon inda take bata yi.





bayan sati guda gimbiya sumayya ce kishingid'e a parlourn ta inda bayinta suke zagaye da ita wasu suna mata tausa wasu fifita,  d'aya tana karanta mata labari, wayartace tashiga ruri baiwar da take rik'e da wayoyintane tamik'a mata, cike da Jin dad'i sumayya tayi picking d'in wayar ko sallama batayiba tace haba zinat ai ni fushi nake da ke wai har ayi aurene bakya garin,

daga chan 6angaren Zinat tace toh sarkin k'orafi yanzu dai gani a k'ofar gidanki dogarawa sun hanani shiga kituro a shigo da ni,

cike da jin dad'i sumayya tace yanzu ko zan aiko,  kallon d'aya daga cikin bayinta tayi ta yamitse fuska tace ke jeki waje kishigo min da bak'uwata,

dasauri tamik'e tace angama ranki yadad'e

batafi minti biyar da fitaba sai gasu sun shigo da zinat,  sumayya tashi tayi daga kishingid'en da take tace oyoyoo k'awata takaina,  nan bayi suka zube suka kwashi gaisuwa wajen wadda aka kira da zinat sai yamutsa fuska take tana taunar chewing gum tazauna saman kujera, nan gimbiya sumayya takori duka bayin daga d'akin,

gimbiya sumayya kusa da ita takoma tazauna kafin kace mi ancika gaban zinat da kayan ciye-ciye da na shaye-shaye, sumayya cike da farin ciki tace k'awata kenan ai ban d'auka zan ganki a yanzu ba,

zinat kur6an ruwan inibi tayi sannan ta aje cup d'in tace wlh jiya nadawo garin shine nace ba zan fad'a mikiba surprise kawai zan baki yau.
.
murmushi Sumayya tayi tace kin ko kyauta wlh, na ma d'auka sai kin gama hutawa zaki dawo domin na sanki da son tafiya kihuta,  zinat tace ai saboda ke nadawo amarya kinsha k'amshi kinga ko yadda kika koma?

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now