Page 4

328 10 2
                                    

tana fita daga d'akin yarima part d'inta tawuce ko ta kan su jakkadiya batabiba da suke tsugunne suna ta kwasar gaisuwa wucewa tayi tashige bedroom d'inta, wayarta tad'auka takira zinat, zagaye d'akin tashiga yi tak'agara zinat tad'aga wayar ammah har tatsinke bata d'agaba,  tsaki gimbiya taja tace itafa matsalata da ita ayi ta kiranta sai taga gama take d'auka,

k'ara Kiranta tayi bugu biyu tad'aga
ko gaisawa basuyiba tace zinat kinajin wancan d'an rainin hankalin wai bazai barni inyi business d'inba

zinat cikin tsawa tace what!  shi har ya isa yahanaki kuma kihanu? gambiya tace hmm yoh ke kina tunanin ma zan hanu?

zinat dariya tayi daga chan 6angaren tace wlh innice yanemi yaraina min hankali tuni zan nuna masa iyakarsa ke ak'arshema zan iya kashe auren tunda dama dashi yake tak'ama,

gimbiya zaro ido tayi kamar tana gaban zinat tace kirufa min asiri ai wlh ba zan iya rabuwa da shi ba saidai nasan ta inda zan 6ullo masa kibarni da shi.

zinat tace toh shikenan nidai ina jira cikin week d'innan inga alert saboda so nake inje ingama komai dawuri indawo,

gimbiya sumayya tace toh shikenan kar kidamu,  nan sukayi bankwana.

suna gama wayar gimbiya ummanta takira saida takusan tsinkewa sannan sultana sadiya tad'aga da sallamarta,  sumayya ko gaisheta batayiba tace ummana wlh yarima baida mutunci

sultana sadiya a rikice tace nashiga ukku shalele miyake faruwa ne?  wlh indai wani cin mutuncin yayi miki zan rufe ido inci masa mutunci shima daga shi har mahaifiyartasa a tafin hannuna suke,  kifad'a min abinda yake faruwa.

Sumayya cike da jin dad'in ganin yadda mahaifiyarta take kula da ita, sannan tabata labarin business d'in da takeso tayi da yadda suka kwashe da yarima.

sultana sadiya tace ai bai isaba Indai ina raye ba zaki ta6a yin kukaba ammah kafin ind'au mataki da hannuna kije kifara samun dada kuyi maganar domin nasan ita zata fahimceki sosai inko ta yarda nasan yarima ma zai amince ko da ace baya so.

cike da jin dad'i sumayya tace hakafa za'ayi ummana wlh saisa nake k'ara sonki saboda duk abinda nake so kema kina sonsa.

'yar dariya sultana tayi tace idan ban so abinda kikeso ba toh nawa zan so? kekad'ai fa ce namallaka,  ke nifa ba ma wannan ba wai har yanzu ba wani bayani?

sumayya ta fahimci inda mahaifiyarta tadosa ammah sai tanuna bata fahimtaba tace ummah wane bayani kuma?

ummanta tace ke gidanku ni zakiyi ma kwana-kwana?  ke ni ban yarda da keba anya bakiyin family planning?

dariya sumayya tayi tace ni babu abinda nakeyi kuma nima insha Allahu sai na shekara biyar sannan zan haihu.

sultana sadiya tace nashiga ukku ke gidanku wa yace miki ana gudun haihuwa a gidan sarauta?

gimbiya cikin shagwa6a tace ummah kema fa saida kika dad'e sannan kika haihu.

ummah tace toh ai nima ba dan ban soba Allah ne bai baniba a lokacin, inma kinsan kina yin wani planning toh wlh kidaina,

gimbiya tace nidai yanzu dai shikenan ummah tunda nace miki babu abinda nake ai sai kibar maganar,  ni nafi buk'atar business d'innan bari dai inje muyi magana da dada, ummah ba dai dan ta yardaba tace toh shikenan sai najiki,

gimbiya tana gama wayar wanka tashiga tayi bayan ta fito shiryawa tayi cikin shigarta gwanin sha'awa sannan tafito nan kuyangi da bayinta suka take mata baya har suka shiga turakar sarki,

lokacin da tashiga parlour dada tana kishingid'e ana mata tausa,  nan duk ma'aikatan dada suka gaisheta tare da yi mata kirari, tana yatsina ta amsa musu,  nan bayinta suma suka zube suka  kwashi gaisuwa a wajen dada,  gimbiya zama tayi gefen dada tagaisheta,

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now