PAGE 12

237 10 0
                                    

Ko da suka isa nan ma maigadi bai hanasu shigaba saboda ya san Rauda sosai.

hango Alh munir sukayi a parking space yana shirin shiga motarsa ganin Rauda tare da zarah yasa yatsaya yana kallonsu fuskarsa d'auke da murmushi har suka iso wajen da yake su dukansu fuskarsu a d'aure take,

Washe baki Alh munir yayi yace Rauda kece tafe tare da sister d'inmu?  ya dai ko itama tana cikine?  ai daman na fad'a miki kud'ine abokan rayuwa nasan daman itama zata amince,  yanzu dai mushiga daga ciki muyi magana ko tafiya zakiyi kibarni da ita?

Rauda cikin fushi tace ni ba wannan yakawomuba nazone in shaida maka ina d'auke da cikinka tsawon wata biyu.

Alh munir saida yafirgita jin ta ambaci ciki ammah yadake yayi 'yar dariya ta rainin wayau yace ciki kuma? Haba kina big gurl ya za'ayi kibari kiyi cikin shege kuma dan kin rainani shine sai kice cikinane?

zarah cike da k'ulewar dariyar da yayi musu tace idan ba cikin ka bane toh na uban wanene?

Alh munir tsagaitawa yayi daga dariyar da yakeyi yace ke kardai kisaki kizageni naga kamar kunya bata ishekiba,

Zarah dariya tayi tace girma dai ya riga da ya fad'i akwai marar kunya bayanka? kabaro iyalanka kazo kana 6ata rayuwar 'ya'yan wasu kuma ciki dole kakar6esa dan baida uba bayan kai.

Alh munir cikin 6acin rai yace baku isa kulik'a min d'an shegeba ita ai tasan wad'anda take bi saitaje tagano wanda yayi mata ciki ammah ni wlh babu wanda ya isa yace cikinane kuma barakiji rauda daga yanzu kar ma kik'ara nuna kin sanni ko da ahanyane, motarsa yabud'e yad'auko kud'i yamik'a masu yace ga wannan kinje kisamu kicire cikin tunda daman kwad'ayi yaja miki sannan kufitarmin daga gida tun kan ranku ya6aci.

Zarah kallon Rauda tayi da taketa aikin kuka ran Zarah ya 6aci sosai, sannan tamaida kallonta ga Alh munir takar6i kud'in tawatsa masa a fuska  tace karik'e kud'inka bama so, eh dole kace haka tunda ka ci moriyar ganga, saidai inaso kasan wani abu kaima kana da 'ya'ya kuma kana da mata dan haka kasaurari naka, kar kamance Allah ba azzalumin bayinsabane kuma fad'an ubanginine abinda kayi sai anyi maka,  murmushin takaici Zarah tayi kwallah duk ta cika mata ido tace alhaki kwikwiyone muje zuwa, rik'o hannun Rauda tayi har sun fara tafiya sannan tatsaya batare da ta juyoba tace kuma ciki ba zamu ta6a zubar da shiba sai ta haifesa anan zamu gane wanene ubansa kuma ko jinin wanene dole mukai ma matarsa tareni cikin shege.

Tana gama fad'in haka taja Rauda suka fita sukabar gidan.

Hankalin Alh munir ya tashi sosai domin tunda yaga zarah yasan zata iya yin komai ma, chan kuma sai yayi murmushi yace naga ta yadda za'ayi inkar6i dan shege, yana gama fad'in haka yakoma cikin gida fitarma yafasa

Suna fitowa Rauda duk'ewa tayi k'asa tacigaba da kuka,  zarah share k'wallar idonta tayi tace yaya Rauda kinga abinda nake guje muku kingani ko yanzu gashinan dukansu babu wanda takar6i cikin kowa ya ce banasa bane.

Rauda tsagaitawa tayi daga kukan da takeyi tace tabbas zarah nagani kuma nasan *NATAFKA BABBAN KUSKURE* da na'amince nabi son zuciyana yanzu gashinan najawo ma kaina babar matsalarma bansan ya zanyi intunkari su mama da cikiba bansan ya zasu d'auki lamarinaba, zarah kawai kitafi gida.


Zarah cike da tausayi tad'ago yayartata daga tsugunnin da tayi tace haba yaya rauda meyasa zakice haka duk abinda yafaru kid'aukesa a matsayin *K'ADDARA CE* kar kidamu nayi miki alk'awali ni zan tsaya miki ga su mama har sai sun fahimceni *KIYARDA DANI* yaya Rauda.

Rauda kallon k'anwartata takeyi cike da gamsuwa ta jinjina kai domin tasan zarah tana da hankali zata iya shawo kan iyayen nasu, share hawayenta tayi tace shikenan Zarah na yarda da ke ammah naga illar abinda na aikata.

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now