PAGE 2

500 17 0
                                    

page 2⃣

Yarima suhail saida yayi kusan minti biyar yana a kwance sannan yabud'e idonsa ahankali yamik'e yasafka daga kan gadon,  alkyabbarsa yajawo yasa batare da ya kalli shahid ba saida yataka yakusan zuwa k'ofa sannan yace kajirani bari indawo,  shahid cike da tsokana yace toh ranka yadad'e

yarima baice komai ba yafita yana tafiyarsa ta k'asaita, dogarawan da suke zaune k'ofar d'akinsane suka zube suna kwasar gaisuwa sannan suka tashi domin sutake masa baya,  yarima batare da ya kallesuba yad'aga musu hannu.

ganin haka yasa duk suka tsaya, yawuce yacigaba da tafiyarsa shi kad'ai duk inda yagifta kwasar gaisuwa akeyi, d'aga ma mutane hannu kawai yake idan da sabo sun saba da halin yarima ahaka har yashiga turakar mai martaba da mamakinsa yaga har da iyayensu a zaune,

waje yasamu gefen maimartaba yazauna a k'asa tare da kwasar gaisuwa wajensa da wajen iyayensu nan duk suka amsa masa, 

maimartaba gyaran murya yayi yace toh Alhmdllh nasan duk zakuyi mamaki akan dalilin taraku nan da nayi ammah ba abun mamakibane alkhairine muke tafe da shi, ba akan kowaba sai akan yarima suhail,

maimartaba cigaba yayi da cewa domin na riga na yanke hukunci saboda nasan zai kar6i abinda nake tafe dashi na alkhairi,  bakomai bane sai akan dubawa da cancantar da naga yayi dan haka naza6a maka matar aure bakowa bace face 'yar uwarka sumayya.

yarima gabansane yaji ya fad'i dasauri yad'ago kai yakalli maimartaba har ya bud'e baki zaiyi magana sai kuma yafasa dan haka yasunkuyar da kansa k'asa tare da runtse idonsa cike da takaicin za6in da maimartaba yayi masa, nan iyayensu sukaita murna suna tofa albarkacin bakinsu akan maganar.

shidai yarima saurarensu kawai yake,

muryar maimartaba ce yatsinkayo yana cewa toh kai uban gayyar bakace komai ba,

yarima suhail kamar ba zaiyi magana ba sai chan yace ranka yadad'e na amshi za6in da kayi min hannu bibbiyu Allah yak'ara tsawon rai.

cike da Jin dad'i maimartaba yace masha Allah, naji dad'i sosai tabbas nasan daman bazan samu matsala daga garekaba wlh ka faranta min nima Allah yakawo lokacin da zan faranta maka,

gaba d'ayansu sukace Ameen, yarima suhail nan yak'ara kwasar gaisuwa sannan yamik'e yafita

umman sumayya kamar tazuba ruwa k'asa tasha saboda murna domin ko bakomai tasan burinta ya kusan ciki ko da taje ma d'iyarta da labarin sumayya har da rawa tataka saboda murna dagudu tafita taje 6angarensu rahama tashaida mata, nan rahama tatayata murna.


yarima suhail yana komawa d'akinsa saman gadonsa yafad'a tare da lumshe idonsa cike da bak'in ciki domin an 6ata masa plan saboda shi baida burin yin aure a yanzu ko ma da zaiyi sumayya bata daga cikin irin tsarin matan da yake da burin aure saidai kawai zai amince ne saboda maimartaba domin baya iya jayayya da shi,

shahid ganin yarima acikin wannan mood d'in yasa bai tambayesa abinda yake damunsaba domin yasan ko da ma ya tambaya toh ba zai samu amsaba saidai idan shi yaso yafad'a masa toh dakansa zai basa labari dan haka yasharesa yacigaba da kallon ball d'insa.

yarima ya dad'e a kwance sannan daga baya yatashi yashige toilet.


bayan sallar isha'i yarima turakar iyayensa yaje inda yatadda mahaifiyarsa kishingid'e wata baiwarta tana mata tausa inda wasu biyu suke gefenta suna mata hira.

suhail yana shiga yatsaya bakin k'ofa ganinsa yasa duk suka zube suna kwasar gaisuwa sannan daga baya suka tashi suka fita suka basa wuri domin yagana da mahaifiyartasa,

sultana bilkisu tashi tayi daga kishingid'en da take nan suhail yataka yaje inda take yazauna sannan yagaishe da mahaifiyartasa cike da fara'a ta amsa masa.

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now