PAGE 9

332 12 3
                                    

Saurayin yaya raudane yashiga lallashinta yace haba baby menene kuma nafad'a a ciki? ni wlh k'anwar ma taki ta burgeni.

Yaya Rauda tace hmm baby kenan bakasan wannan yarinyar ba ai kwata-kwata ita ba wayaiya bace.

murmushi yayi yace har ina shirin ince ina ciki.

wani irin kallo Rauda tayi masa tace k'anwar tawa?
murmushi yayi yace eh man toh menene?

Rauda ta6e baki tayi tace ai wlh ba zai yuwu kajefi tsuntsu biyu da dutsi d'ayaba dan haka abar ma maganar nan baby,  yanzu idan katafi sai yaushe zaka dawo?

cije le6e yayi tare da jingine kansa a sit d'in da yake zaune sannan yace 1 week kawai zanyi cike da tsokana yace kinsan matata kwana biyu nayi missing d'inta.

Rauda d'aure fuska tayi tace haba Alhaji Munnir wai meyasa kake min irin haka.

murmushi yayi yace sorry dear kinsan akwai aikin da zanje inyi, yanzu dai fatana kikular min da kanki har indawo.

Rauda tace kar kadamu dear insha Allahu zaka dawo kasameni yadda kabarni,

murmushin jin dad'i yayi yace yauwa baby nagode, 10k yad'auko yamik'a mata yace ga wannan kirik'e kafin indawo,

Rauda kar6a tayi tace nagode baby Allah yamaido min kai lafiya
yace Ameen dear,  nan sukayi sallama.

Rauda ba ko sallama tashiga gida kallon zarah tayi da take hura wuta tace ke ina ledar da nace kishigo min da ita?
zarah batare da ta kalli Rauda ba tace tana d'akinmu, Mama da take cikin d'aki jin muryar Rauda yasa tafito tana washe baki tace a'a 'yar albarka ashe kece kika dawo, tun jiya muna ta zuba ido ammah shuru.
Rauda yamitsa fuska tayi tace ammah mamanmu kinsan dai duk ma inda naje toh zan dawo.
Mama tace hakane saidai duk abinda kuke nafison inganku kun dawo gida komai dare kun kwana.

Yaya Rauda batare da tace komai ba tawuce tashige d'akinsu.

wannan 'yar maganar da mama tayi zarah taji dad'inta sosai domin duk abin mama toh tanaso taga yaran nata sun kwana a gidansu, saidai duk maganar da zatayi musu Yaya Rauda idan tasa kanta waje take kwana,  idan ma iyayen sunyi magana sai tabasu kud'i tarufe bakin.

Mama kallon zarah tayi tace tashi kije kikar6o min 500 wajen Rauda kizo kisiyo taliya a Zuba naga ruwan ya kusan tafasa,
zarah tace toh mama.

tana shiga d'akin kallon Rauda tayi da take shirin shiga wanka tace Yaya Rauda mama tace kibada d'ari biyar asiyo taliya.
Rauda tace mik'o min jakkata, zarah zuwa tayi tad'auko jakkar tabata nan Rauda tamik'o mata kud'in sannan tashige wanka.

Zarah wajen mama tadawo tace mama guda nawa za'a siyo.
Mama tace siyo biyu sai kikawo min canjin,  zarah tace toh sannan tatafi.


_*After 2 weeks later*_

Zarah ce zaune tana tsifar kanta, wayartace tashiga ringing nan tad'auko ganin sunan malam Bello da yabayya a screen yasa tayi picking tare da yin sallama,
daga chan 6angaren ya amsa mata, nan suka gaisa,  sannan malam Bello yace dear gani a k'ofar gidanku kifito inganki please.
zarah jim tayi nad'an lokaci sannan taduba agogo taga k'arfe biyar d'in marece. muryasa taji yana cewa zarah ya kikayi shuru ko bakiso nazoba?
zarah tace bahaka bane malam gani nan zuwa batare da tajira jin abinda zai ce ba takashe wayarta,

nan ta tufke kanta da ribbon sannan tajanyo hijab tasaka saida talek'a ganin ba kowa tsakar gida yasa tayi hamdala sannan talalla6a taficce.

A k'ofar gida tasamesa tsaye ya zuba ido domin yaga ta ina zata fito, suna had'a ido dasauri zarah taduk'ar da kanta k'asa tare da yi masa sallama.

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now