PAGE 19-20

732 39 15
                                    

*PAGE* 19

ummi kiran mama tayi a waya lokacin mama tana zaune tsakar gida ita da abbah suna cin abinci, mama jin wayarta tana ringing yasa tad'auko ganin sunan sultana bilkisu da yabayya yasa tazaro ido tare da cewa malam sultana ce take kirana.

Abbah yace toh toh d'aga muji abinda zatace, mama saida ta saita nutsuwarta sannan tayi picking d'in call d'in tare da yin sallama.

daga chan 6angaren sultana bilkisu ta amsa mata cike da fara'a, nan suka gaisa cike da girmama juna, ummi tace ya su zarah dafatan duk suna lafiya?
mama tace lafiya lou, nan ummi take shaida mata akan maganar neman auren zarah da za'a zo gobe.

mama kallon abbah tayi da yake sauraren firar tasu,  alama yayi mata da tace toh.
mama tace toh ranki yadad'e Allah yakaimu.
cike da jin dad'i ummi tace Ameen mungode sosai, ammah idan mahaifinsu yana kusa kiban shi inaso muyi magana inkuma baya kusa idan yadawo zan kira,

mama tace ranki yadad'e yana ma kusa gashi, nan tamik'a ma abbah waya.

Abbah kar6a yayi tare da yin sallama nan suka gaisa cikin mutunta juna,  sultana bilkisu tace yauwa daman akan tsaida rana ne agaskiya mu a Royal family d'inmu ba'a yin baiko ad'auki lokaci shine nakeson in rok'eka alfarma dan Allah kar asa lokaci dayawa,

Abbah Jim yayi yakasa cewa komai.
sultana bilkisu tace kayi mamakin jin haka ko? kuyi hak'uri wlh tsarin masarautarmu ne haka.
Abbah cike da damuwa yace ranki yadad'e gaskiya hakan bazai yuwuba domin mu ba halinmu d'ayaba idan mukace ayi bikkin cikin gaugawa toh gaskiya zamu cutu tunda bamu fara tara komaiba da dai ataimaka asa ranar da d'an nisa domin musamu muyi mata abinda Allah yahore mana.

daga chan 6angaren ummi murmushi tayi tace kar kadamu ni zan d'aukema zarah duk wani abu da iyaye yakamata suyi ma 'ya'yansu wlh ko da ba d'ana zata auraba zan iya yi mata haka.

Abbah yace a'a ranki yadad'e kar hidimar tayi yawa kibari dai zamuyi.

ummi tace kar kadamu tunda nace zanyi kubarsa kawai wannan yazama sirri tsakanina da ku domin bana fatan wani yasan da hakan saboda gori da wulak'anci

maganarta tayi ma abbah dad'i sosai ganin yadda take Royal Family ammah bata d'auki kanta komai ba tasan abinda yadace da wanda bai daceba, muryar sultana bilkisu yaji tana cewa bawai ina nufin naraina k'arfinkuba wlh ko d'aya ko da ace ba zarah bace zan iya yi ma wata barema zarah da zata auri jinina dan Allah ka amince ma buk'atata a karo na biyu, malam yace toh ranki yadad'e mungode sosai Allah yabiyaki da gidan Aljannah,
ummi tace Ameen nice da godia da kuka amince min sai kunjimu, agaishe da su zarah.
malam yace haba bakomai ranki yadad'e, su zarah zasuji.

bayan sun gama wayar Mams kallon Abbah tayi tace malam toh yanzu ya za'ayi? wannan neman aure ba ko  shiri.

Abbah yayi murmushi yace gaskiya mutanen nan suna da kirki sosai bamuda abinda zamu biyasu da shi saidai muyi musu addu"a.

mama tace hakane da ace haka masu kud'i suke da ansamu sauk'in wani abun ammah yanzu sai kaga maikud'i sai d'iyan masu kud'i, Hajiya da Alhaji, d'an malam Audi me goro sai 'yar Malam idi mai icce, bakowane iyaye suke amincewa 'ya'yansu su auri 'ya'yan talakawa ba,
Abbah yace hakane abun ne yanzu sai addu'a domin masu son talakawa suna ra6arsu basuda yawa wani lokacin ni abun har mamaki yake bani ince toh wai su mancewa suke da Allahn da yabasu zai iya amshewa a duk lokacin da yaso? ko suna mancewa Allahn da ya azurtasu shine yayi talakka kuma ba dan baya son saba, ko suna mance fad'arsace cewa shi yake azurta wanda yaso yakuma hana wanda yaso, Allah dai yasa mudace.

mama tace Ameen y rabb.
Abbah yace toh yanzu sai kurubuta duk abinda kuke buk'ata na tarar bak'in sai insiyo muku, ko kuma kuta6a kud'in nan kud'ibi yadda zasu isa kuje kasuwa yanzu kusiyo abinda kuke ganin ya dace dan ni yanzu fita nakeson yi zan ma biya gidan yaya manu inshaida masa dan yasan da zuwansu gobe yashigo da wuri,

You've reached the end of published parts.

⏰ Last updated: Jul 26, 2020 ⏰

Add this story to your Library to get notified about new parts!

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now