PAGE 16

265 9 0
                                    


Page 1⃣6⃣

Sultana Bilkisu ko da takoma gida cike da farin ciki tasamu Sultan Ahmad take bayyana masa yadda sukayi da iyayen zarah, shima farin cikinsa yanuna a fili yace gaskiya naji dad'i ammah kuma ba'a nan takeba,

murmushi sultana tayi tace nasan kana tunanin matsalar da zamu fuskantane wajensu memartaba da yarima?

Sultan Ahmad shima murmushi yayi yace tabbas hakane ammah Insha Alkahu komai zaizo da sauk'i kibani lokaci nima inyi tunanin yadda zamu 6ulloma lamarin domin maganar nan tana buk'atar tunani mai zurfi a cikinta.

Sultana Bilkisu Cike da damuwa tajinjina kai tace hakane nima zanje inyi tunani domin musamo mafita.

Sultan Ahmad tausayin matarsa yakamasa domin yasan yadda take son d'an nata, yace kidaina damuwa indai Allah ya k'addara akwai aure tsakaninsu toh za'ayi inkuma babu toh hak'uri zamuyi domin wani baya auren matar wani fatanmu dai Allah yashige mana gaba.

Sultana Bilkisu cike da gamsuwa da maganar mijin nata tace Ameen.



Gimbiya sumayya duk yadda taso tadaure kar tabada kanta ga yarima ammah kasawa tayi a daddafe tayi kwana biyu.

bayan sallar la'asar shiryawa tayi sosai tafito tanufi 6angaren yarima tana shirin shiga sai gashi ya fito da alamu fita zaiyi, kallo d'aya yayi mata yad'auke kai yana shirin ra6awa ta gefenta yawuce dasauri Gimbiya Sumayya tasha gabansa tace haba yarima wajenka fa nazo.

fuskar yarima babu alamun fara'a yace me zanyi miki?

Gimbiya kallonta takai ga dogarawansa da guards d'insa da duk kansu yake sunkuye suna jiran ogan nasu, ga kuyanginta da suke bayanta tsaye, kallonta tamaida ga yarima tace am daman, nan tafara kame-kame tace ko dai zamu shiga...... Yarima hannu yad'aga mata yace whatever ma dai  you should meet me later, bai jira jin abinda zataceba yawuce dogarawan da guards d'insa suka take masa baya.

Gimbiya sumayya takaici duk yacikata ganin yadda yarima yadisgata gaban guards d'insa hararar kuyanginta tayi da kansu yake sadde a k'asa tacemunafukai kun zuba min na mujiya duk sai nad'au mataki a kanku.

dasauri duk suka zube k'asa suna cewa Allah yahuci zuciyar gimbiya, Allah yaja da ran gimbiya.

wucewa tayi fuu dasauri suka tashi suka take mata baya sunayi mata kirari.

ko da takoma part d'inta saman gadonta tafad'a tare da dafe kanta tsaki taja tace wannan mutumin bansan irinsaba anya yarima bai fara bin mataba? ya za'ayi yad'auki tsawon wannan lokacin batare da maceba? gabantane yashiga fad'uwa cikin d'aga murya tace No! i dont think yarimana akwai macen da zai iya kulawa wlh ba halinsa bane, chan takaima katifa bugu da hannunta tace inma akwai zan bincika domin nasan yarima baya iya kai tsawon wannan lokacin without ya yi making sex da niba ko da ace bana so, inma har naga akwai wadda yake tare da ita toh wlh ba zan bartaba sai na kasheta!!! 

wayarta tajawo takira zinat bugu biyu tad'auka, muryar sumayya tana rawa tace wai ke zinat yaushe zaki dawo k'asarnan?

dariya zinat tayi tace kinyi missing d'ina ko? 
tsaki sumayya tayi tace ke ni tambayarki nake.

zinat murmushi tayi tace Allah yahuci ran gimbiyar yarima very soon zan dawo nima ai nayi missing d'in k'asata.

Sumayya tace hmm Allah yasa dagaske kike, nidai in kindawo kifara biyowa ta wajena.

'yar dariya zinat tayi tace sai kin ganni, sumayya dai badan ta yadda da maganar zinat ba takashe wayanta tare da komawa takwanta tana sak'e-sak'e cikin ranta.


Da daddare ganin ta kasa bacci yasa tamik'e tajawo alk'yabbarta tad'aura saman kayan baccinta tafito batare da ta nemi rakiyar kowaba tanufi 6angaren yarima addu'a take Allah yasa kar yadisgata domin ita tasan yau duk wulak'ancin da zaiyi mata ba zata damuba Indai zai biya mata buk'atarta inyaso daga baya sai tarama.

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now