PAGE 15

239 6 0
                                    


page 1⃣5⃣

Malam musa yace gaskiya ba zamu iya amincewa da buk'atarkiba domin kunfi k'arfinmu ku masu kud'ine mu kuma talakkawane, kinga ba zaiyuwuba ace masu sarauta kamarku sun had'a zuri'a da muba.

sultana bilkisu tace kar kudamu ai anzama d'aya kar kumance da talakka da maikud'i duk Allah ne ya haliccesu kuma shi yakeba Wanda yaso yahana wanda yaso, jahiline kawai zai iya gudun talakka, ammah duk wanda yasan abinda yakeyi toh ba zai gujesaba domin yasan wake azurtawa da hanawa,  a lokaci guda Allah zai iya maida talakka mawadaci sannan yamaida mawadaci talakka, toh tayaya kuke tunanin zamu gujeku? saidai idan kuna tunanin d'iyarkune kar mucutar da itane, insha Allahu ba zamu nuna banbanciba zamu kula da ita kamar yadda zamu kula da 'ya'yanmu da muka haifa a cikinmu, burina kutaimaka ku amince kubamu auren zarah.
mu musulmaine munsan girman alk'awali dan haka nayi muku alk'awali zamu kula da ita bakin gwalgwado.

gaba d'ayansu shuru sukayi suna saurarenta,  yanayin yadda sultana tayi maganar yasa suka yadda da ita, kuma sunsan adalci da kirki irin na sarkin garin indai shi zuri'arsa suka biyo mutunci toh ba zasu samu matsalaba.

chan Abbah yakalli mama yace tataso suje suyi shawara dan haka mama tatashi suka shiga d'aki suka bar sultana zaune wajen tana dannar waya, 

a chan d'akin abbah yakalli mama yace zainabu abun nan yad'aure min kai kina ganin zai yuwu mubasu d'iyarmu? nifa ina tsoron su wulak'anta mana ita domin su masu arzikine mukuma talakkawa.

mama jinjina kai tayi tace nima abinda nake tunani kenan gaskiya kar mubasu domin bamusan yadda gaba zata kasanceba, ace duk matan garin nan surasa wadda zasuce sai zarah, so suke sujamana zagi da surutun mutanen gari.

malam musa jinjina kai yayi yace ni bama dai wannan ba kiduba kiga bayanin da tayi mana tabbas daga gani tasan daraja da mutuncin mutane daga jin kalamanta, ta ni bandamu da surutan mutaneba saidai inajin tsoron su  wulak'antamin zarah domin yarima suhail ya wuce ajin zarah wajen komai, ammah kuma ina jin nauyinta bana iya hanasu zarah.

ummah tace hakane malam ko dan matsayin da darajar da ke garesu kaduba kaga bata nuna mana k'yamaba nima wlh ta wajena babu matsala domin halayyarta ta yi min kuma nasan indai d'antane takeson hadawa da zarah toh bamuda matsala saboda da alama zai kasance mai irin kyawawan halinsu saidai ba a nan takeba matsalar tana wajen zarah.

malam musa jinjina kai yayi yace tabbas zarah itace matsalar ina tsoron taki amincewa saidai nasan zarah akwai biyayya zata iya bin ra'ayinmu ko da ace bataso, dan haka idan kinga hakan ba matsala toh muje mu amsa mata,

mama tace toh nan tabi bayan malam musa suka fito, yadda sukabar sultana haka suka dawo suka taddata, suka koma mazauninsu suka zauna.

kallonsu sultana tayi tace dafatan kun yanke hukuncin da kuke ganin ya dace wlh Indai baku aminceba zamu iya hak'ura domin ta yuwu zarah ba matarsa bace.

malam musa yace ranki yadad'e mun ma amince domin darajarki da martabanku yasa bama iya ji zamu iya hanaku zarah fatanmu dai zaku rik'eta kukular mana da ita tsakani ga Allah.

sultana bilkisu tunda taji ya ambaci sun amince wani irin farinciki yakamata kasa 6oye murnarta tayi tace gaskiya naji dad'i kuma nagode sosai insha Allahu zamu kular muku da ita, sannan zanje muyi magana da iyayensa koma dai mekenan zamuyi waya, takalli mama tace bani number d'in wayanki nan mama takaranto mata sannan sultana bilkisu takira kuyanginta suka dawo, fuskarta d'auke da fara'a tace naso ace naga d'iyartawa ammah tunda batanan zamu had'u wani lokacin.

mama tace a'a ranki yadad'e ai sai inje inkirata tana chan bayan layin nan sunje kitso,  sultana tace a'a kibarta kawai zamu gaisa wani lokacin, kar6ar jakkarta tayi a wajen d'aya daga cikin kuyanginta tazaro 100k ta aje musu sannan tamik'e tace bari inwuce.

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now