PAGE 8

298 13 0
                                    

tashi tayi fuuu tawuce tabar d'akin tana mita ita dai zarah bin rauda tayi da kallo cike da bak'in cikin halin 'yan gidansu a kullum addu'anta Allah yasa sugane gaskiya.

addu'a tayi sannan tatashi tacire hijab d'inta tafito takar6i kayan miyan da suke hannun mama tajajjaga mata sannan tatambayeta idan akwai abinda za'a,  mama tace a'a,
sannan tawuce takoma d'aki koda tayi sallar isha'i zama tayi tana ta bitar karatunta sai wajen k'arfe takwas sannan k'anwarta Aysha tadawo gida hannunta d'auke da leda tun daga zaure tafara kwalah ma mama kira

mama da take tsugunne tana hura huta jikinta yana 6ari tamik'e tana washe baki tace a'ah autata har kin dawo.

Aysha tana yatsine fuska tace eh wlh ,
mama kar6ar ledar hannun Aysha tayi tace me kuma muka samu?

Aysha kar6e ledarta tayi tace kai mamanmu ba fa wani abu bane d'inkinane nabiya na amso,

fara'ar da take d'auke a fuskar mama ce taragu tace kina nufin babu abinda kika kawo mana?  kiduba kiga 'yar uwarki kaza takawo mana gata chan saman wuta ina mana ferfesu,

Aysha tace oh mama kedai kullum burinki abaki kud'i, jakkarta tabud'e tad'auko 2k tace gashinan kid'auki d'aya kiba abbah d'aya.

mama kar6a tayi tana washe baki tace kai 'yar albarka gaskiya naji dad'i ammah ba zan ba mahaifinkuba dan shima d'azun ya samu kud'i kar ma kikuskura kifad'a masa kin bamu kud'i,  Aysha wucewa tayi tanufi d'akinsu tana cewa nidai mamanmu wannan tsakaninku da abbane,

zarah tana zaune saman darduma tana sauraren dukkan abinda suke tattaunawa,

Aysha ce tashigo d'akin tana cewa wash wlh na gaji, jafe jakkarta tayi bisa katifa takalli zarah tace yaya zarah kina nan kina ta bitar karatun?

zarah batare da takalletaba tace Aysha daga ina kike?  meyasa kikeso kiga kinyi dare a waje a matsayinki na mace?

Aysha turo baki tayi tace ammah ai mama tasan da tafiyata,  zarah aje littafin da yake hannunta tayi tare da tattara dukkan hankalinta ga k'anwarta tace Aysha wannan rayuwar da kika d'aukar ma kanki ba mai 6ullewa bace k'ara tun wuri kigyara tun kan lokaci yak'uremiki gudun kar kiyi nadamar da batada amfani.

mama ce da tazo wucewa tajiyota tana magana lek'owatayi d'akin takalli zarah taharareta tace toh sarkin 6akin ciki mekike ce mata? badai hure mata kunne kikeyi ba dai ko? 

zarah kallon mama tayi tace a'a mama kawai ina bata shawarace d's zata fisheta.

salati mama tahau yi tace nashiga ukku ni Zainabu yau Allah yabani d'iya mai bak'in ciki da ni, yanzu 'yan kud'in da take kawo mana ne kike ma bak'in ciki?  toh idan suka zauna gidan ubanwa zai dinga ciyar da mu? kinsan dai mahaifinku bai bada abinda zamu ci muk'oshi .

zarah cikin lallashi tace mama kiyi hak'uri ni ba haka nake nufiba, idan na 6ata miki rai kiyi hak'uri.

mama tace daman ai haka zakice munafuka kawai wlh da ace ba ni nahaifekiba da na ce ke ba jinina bace.

zarah dai shuru tayi tana sauraren maganganun mama har mama tagama fad'anta tafita tabar d'akin.

karatunma zarah kasa cigaba tayi saboda haushi nan ta tattare littafan tamaida su ajakkarta,  sannan tahaye saman katifarsu takwanta.

Aysha wanka tayo tashirya akan idon zarah wani yakirata a waya tafita tabar gidan, 'yar nokianta ce da taji tana ruri yasa takai idanunta a wajen ganin wanda yake kiranta saka tayi murmushi har dimples d'inta suka lotsa cike da farin ciki tayi picking domin tasan ko bakomai Malam Bello zai d'ebe mata kewa sallamata tayi masa,  shima cike da farin ciki ya amsa mata,  bayan sun gaisa malam Bello yace gimbiya zarah ya gida? 

YARIMA SUHAILWhere stories live. Discover now