page 14

2.8K 200 3
                                    

*🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

*wannan shafin nakine mom humaid*

14

Wuraren k'arfe uku na dare ta farka,mamakin take sanda tazo jikinshi har haka,fitsari takeso tayi amma ta kasa koda motsi sabida yanda d'imin jikinshi ke saukar mata da kasala,a hankali ta ce "Yaa Abdul ka d'aga ni ina so zanje bathroom ne" be motsa ba sanda ta maimaita so kusan uku sannan ya bud'e idonshi a hankali ya sakar mata lallausan Murmushi dukda acikin duhu suke,hannu yakai ya kunna side lamp dake d'akin sannan ya sake riqon daya mata yace "Sorry na hanaki tashi bacci ne yamun nauyi" Mik'ewa tayi kurun ta gyara gashinta daya yamutse taje toilet d'in tayi fitsarin ta dawo,zaune ta taddashi tace

"Lapia dai yaa Abdul?" Murmushi ya sakar mata " Ai komai Nisan dare idan aka tashe ni bana iya komawa baccin " b'ata fuska tayi tace "Ohhsh Allah dana sani ban tashe kaba wlhy,yanzu haka zaka yita zama kenan??" Kishin gid'a yayi yace parlor zanje inyi kallo kawai" zaunawa tayi kusa dashi tace "To nima zan bika muyi kallon tare"
"Noo plss karki damu,ki kwanta kiyi baccin ki kinji" mak'e kafad'a tayi "ehmm ni bazan kwanta d'inba zanje mu zauna tare kawai" Mik'ewa yayi yace "if u insist" Murmushi kurun tayi tabi bayanshi,Jennifer's diary yake kallo dai itad'ima zama tayi se dariya sukeyi sabida anata yin abin dariyar,bacci ne yafara fizgarta,ganin tana d'ingishi ya sanyashi dariya ya janyota jikinshi kanta ya datura akan cinyarshi yashiga Shafa lallausar sumanta "Kiyi bacci Hafsat,bacci kikeji naga alama" batayi musuba tashiga lumshe ido,har cikin ribs nata take receiving saqonnin dayake aika mata,a haka bacci barawo ya kwasheta,gogan shima a zaune yayi baccin basu suka farka ba se 7 wannan ma ita d'ince ta fara farkawa k'urawa fuskarsa ido tayi tana mamakin kyakyawar fuskarsa har acikin bacci,tana so ta tasheshi yayi sallah,taga alama ma kwanciyar na bashi wahala sosai sabida a saman kujera kanshi ya tafi sosai kasancewar a k'asa suke,tuna wa tayi da yanda Husnah ta koyar da ita yanda zatana tashin mijinta a bacci,Murmushi tayi aranta tace zan iya kuwa?? A hankali ta tashi daga jikinshi ta sanya hannunta tana Shafa kanshi a hankali,bud'e idonshi yayi ya sau kesu a kanta,da Murmushi ta tare shi tace "Kayi Latin sallah yaa Abdul ka tashi" Mik'ewa yayi a hankali batare da yayi magana yabar gurin, itama ta miqe tawuce d'akin ta,wanka tayi ta shirya tsaf cikin wata doguwar riga mara nauyi me santsi da kyawun gaske kalar sararin samaniya ta tufke gashin kanta a tsakiya tayi masa style na donut, ta feshe jikinta da turaruka dama gashi tayi wanka da ruwan miski se tashin k'amshi takeyi tako ina. Parlor tafito har wannan lokacin be dawo ba,se can ya shigo cikin Shiga ta kananun kaya riga da wando,wandon jeans blue sa shirt kalar sararin samaniya shima yayi kyau matuka se tashin k'amshi yakeyi,zama yayi kusa da ita yace yana mai janyo hannunta

"Ur looking beautiful Elham" Murmushi tamasa tace "u too" hancinta ya d'an ja "ohh Really?" Langwab'e kanta tayi tace "yea Kayi kyau sosai,ko wurin budurwar ka ta nan k'asar zakaje?" Murmushi yamata yace "Ai itane zatazo karki damu da wannan" cikeda isa ya nuna wannan,gabanta ne ya yanke ya fad'i ta yi Murmushi tace "zanji dadi idan na ganta kuwa" kallonta kurun yayi ya mik'e ya bar wurin......

Rayuwa tayiwa Elham k'unci kasancewar tunda sukazo bata sake saka Abdul a idon taba tun kwanan farko, tsoro me tsanani ya shigeta,gashi se yan matan turawa masu masa aiki take gani suna kai kawo a part d'in shi,takuma tambayi d'aya daga cikinsu inda yake tace mata fitar asuba yakeyi ya dawo late,yau kusan kwananta shida kenan bata ganshi ba abinda ta rasa amma batajin dad'in rayuwarta sam!!! Ganin ya Shigo da sauri ta miqe taje gunshi "Yaa Abdul lapia kuwa? Kwana biyu bana ganinka?" Hannunshi ya sanya ya tureta yace cikin maye "Zaman uwarki nake a garinnan dazakice Sekin ganni kullum,wlhy ki Shiga taitayinki" zaro ido waje tayi jin muryarshi se a sannan ta kula da yanayinshi sarkace k'atuwa a wuyanshi da wando iya gwiwa daka ganshi kaga zararre kuma a buge yake,kafin tayi wani yunkuri ya fad'o ajikinta,tare shi tayi sannan cike da k'arfin hali taje ta kwantar dashi a d'akin shi,wannan ne karo na farko data fara Shiga d'akin kuma ya tsoratar da ita, ko ina kwalaben giya ne da kwalayen sigari,bata tab'a zato cewar yana aikata wannan mugun abin ba,tausayin momy ne ya kamata tace a sarari murya na rawa "Wlhy nikan nashiga uku na,ya Allah ka kawo mun agaji" anan ta durqushe ta rushe da kuka me ban tausayi,kome yasa takejin tausayin Abdul oho...Tunawa tayi da yanda akeyi cikin films idan mutum yasha giya da sauri ta Shiga toilet nashi ta dauko towel da ruwan sanyi masu ice tazo tana Shafa masa akai a hankali,sanda ta kula yafara sound and safe sleep sannan ta kwanta a kusa dashi taci gaba da kukanta,bata masan me take wa kukan ba,wani abu takeji me d'aci har cikin ranta a wannan lokacin,a haka bacci ya kwasheta,se yamma ya farka tsoron abinda yayi ne ya dawo masa akai ganinta ajikinshi ya tariyo masa komai,dafe kanshi yayi yana kuka me sauti wanda kukanne ya tasheta,k'ura masa ido tayi sanda yayi me isarsa sannan ta dafa kafadar shi tace "Yaa Abdul dan Allah ka dena kuka" jiyowa yayi ya kalleta da jajayen idonshi yace "Hafsat dan Allah ki yi hakuri kuma ki rufamun asiri karki gayawa Su momy,wlhy bana neman mata giyar ce kawai kuma zan dena I promise" k'ura masa idonta tayi se hawaye kasa cewa tayi da shi komai,ta zauna zaman kuka awurin,janyo ta yayi ajikinshi yace "Hafsat ki tallafi rayuwata na dena shan giya,wlhy ba laifi na bane,nace dasu banson sarautar nan nafi buk'atar rayuwata cikin kwanciyar hankali amma sun kasa ganewa wlhy Hafsat bana so,zumunci yaqi saidai tuwa sabida sarauta,d'an uwa na neman ran d'an uwansa sabida sarauta,inaso na auri Humaira sun hanani sabida munafuncin sarauta,yanzu sun k'ara rabani da Raihan sabida nasu ra'ayin,Elham ki yarda dani banida burin tarwatsa rayuwar ki shiya san ya na gujewa aurenki bansan kalar muguntar dazasu miki ba, karkema Su rabaki da farin ciki na har abada,Hafsat wlhy na rantse miki banaso ki Shiga damuwa akaina,Banso ko kad'an kika zama cikin wayanda zasu d'and'ana muguntar gidan sarautaba" kasa magana tayi ya d'ago kanta ya sanya duka hannayenshi ya d'ago kanta ta hanyar Saka lasu a cheeks nata ta fuskance shi

"Hafsat ki yarda da zancena nafi shekaru biyar ina d'awainiya da sanki cikin raina,wlhy Humaira da Raihan duk badan sun zamemin dole nake san auren suba, sabida kurun sud'in yan gidana,I really don't wannan drag u and ur family in to this mess,naso sosai kiyi aurenki inda zaki huta,momy ta kasa fahimta na,akanki kisane kawai bazan iya ba wlhy bazan juri ana neman tab'ar b'are rayuwar ki ba,ki sani ina sane nake zaginki nacin zarafi sabida kawai ki ce bazaki aure niba dan kisamu freedom me dorewa,ko bayan auren mu danake zaginki dan kawai ki kasa daure wa ne kice bazaki zauna daniba ki huta,ban tab'a zaginki Nayi bacci ba wlhy Hafsat duk sanda naci zarafinki bana iya bacci, sabida bakin ciki ni kanji natsani kaina amma ya zanyi.Tsakanina dan iyayenki biyayya ce me tsafta ki binci kesu kiji,tun ranar da muka taho yau gobe nakejin wasu maganganu daga gida wayanda bazan jura ba,Hafsat zan sauwaqe miki sabida inasan ki dauwa ma a farin ciki badan komai ba,idan ba wannan hukuncin na yanke mana ba wlhy bazasu barki ba Hafsat,sannan kuma bazan tab'a yin bankwana da giya ba idan nace zan rayu dake kina shan wahala,kuma soyayyar kice Zata halla kar dani idan har ban rayu dake amma na sani bakya sona ni kuwa farin cikinki shine nawa,sabida haka zamu rabu Hafsat ki guji yan gidan sarauta,anmiki asara mafi muni a yanzu haka,zuwa next week zan maidaki gida" k'ura masa ido kurin tayi takasa koda k"wak'waran motsi,Mik'ewa yayi yaje ya bud'e wardrobe d'in sa ya d'auko takarda ya miqa mata takardar yace "karanta kigani Hafsat,kuma kar kiga laifina koku zargeni wlhy k'aunace sila,kuma koda kin koma gida dan Allah ki guji faruk wlhy har cikin raina nakejin wannan tab'in dayake wa jikinki" Mik'ewa tayi jikinta se rawa yakeyi ta kasa bud'e takardar illah kallonshi kawai da takeyi cikin rashin fahimtar zancensa, janyota yayi jikinshi ya rungumeta sosai ya saka wani razanannen kuka daya tayar mata da hankali......

Hmmm to wai jama'a meyake damun Abdul,abin zantuttukan hankali yakeyi kuwa? Anya tun farko bamu kasa fahimtar Abdul ba kuwa? Muje zuwa dai kuna tare da alkalamin mom Nu'aiym

Hafsat ElhamWhere stories live. Discover now