page 12

2.9K 229 1
                                    

*🌞HAFSAT ELHAM🌞*

Billy Galadanchi

Haske writer's Asso💡

Vote me on wattpad@68billygaladanchi.
Sadaukar wa ga k'awata Hafsat Abubakar qaya (Elham).

*Wannan shafin nakine Lil sis queen Miemie,Allah ya albarkaci rayuwar ki Ameen*

12
A d'akinta takasa yin kuka, tunanin irin rayuwar datakeyi da Abdul take tana mejin tsoron kalar zaman dazasuyi idan har tabar k'asar ita dashi kurun, sukuku ta wuni ranar ba karamin tashin hankali take cikiba,da magrib suka shirya zuwa gidan a b'angaren momy suka sauka,kayakyawar tarba tamusu,sunsha hira ko wannensu ya ware ya nunawa momy ba matsala a tsakaninsu,daganan suka wuce part d'in Fulani Habiba then suka wuce part d'in me martaba, ya musu Nasiha sosai akan zaman lapia da mutun ta juna kuma sun d'auka har zuci agabanshi,koda zasu tafi sarqar gwal ya baiwa Elham dalleliya me dauke da zobuna da awarwa raye,ta zuba godiya ba adadi sannan suka fito kai tsaye wurin mota ya nufa da ita sanda taga da gaske yake sannan tamkar zatayi kuka tace "Yaa Abdul bamuje mun gaisa dasu Innah da Baba ba" wulakance ya kalleta
"Au Baba me gadi wai,ina kinga da kanshi ya gaidani sanda muke shigowa kuma ai shine ya bud'e mana gate sabida duty d'insa ne,Kedai daki kaga ya dace ki gaidashi kije bazan hanaki ba,amma ni shi yake gaidani kuma Kema kin shaida hakan" wani bak'in cikine ya tarnak'owa Elham har wani d'aci takeji acikin yawunta haduye yawu tayi masu zafi sannan tace "Na sani ai Yaa Abdul bata yanda za'ayi me mulkin duniya ya gayar da me gadi,dama bance ka gayarda me gadi ko matar saba, amma y'ar me gadi ita ai tasan darajarsa kamar yanda tasan iyayen kowa,ta sani Babba babbane,sabida koba dan sun haifeta ba dole ta girmama Su" tana kaiwa nan ta juya,shi kuwa ya k'ura mata ido yana nazarin kalamanta....gaskiya Abdul akwai mugun hali,suk kalar zugae da khamis ke masa ai shima yanada hankalinsa be dace yanawa Elham haka ba....

Bayan kwana d'aya suka cira zuwa Lagos,har suka shirgi ba mewa kowa magana, ita ykamma tunda yaqi zuwa gaida iyayenta bata k'ara koda gaidashiba shikuwa ya nuna mata ko'a jikinshi,Suna hawa hanya gogan ya soma bacci ya daura kanshi a saman kafadarta,acikin baccin ya daura dayan hannushi saman cin yarta,ita dai batayi kokarin hanashi ba a haka har suka yi landing, hannunta ta saka tad'an bubbuga cibyarshi firgigit ya farka ganin shi ajikinta ya sanya duk yaji nauyi,shine ya rigata Mik'ewa yace muce, a hotel suka sauka d'aki d'aya ya kama musu badan yasoba,sedan yayiwa momy alk'awarin bazewa mamanta nisa ba har abada, Suna Shiga ta wuce Bathroom sabida ta gaji towel nata ta dauka a jaka yana kallonta tashige labulen d'akin ta daura towel d'in ta dabe wuce duwawu kadan ba,ta fito ta shige wankan,tana fitowa tazo Shafa mai,koda take zuwa ya dawo dagashi se gajeren wando,girjinshi faffad'a ga wani yalwa taccen lallausan gargasa kwance luf a ilahirin jikinshi se sheqi sukeyi,farar fatarsa ta kara nuna wa acikin bakin gashin tayi luf luf a jikinshi,gabanta ne yayi mummunan wannan karo na farko data fara ganinshi a haka,dan sauri ta dauke kanta tazo tana Shafa mai,haka kurun yaja mata tsaki yace

"Ke menene haka? Meye na zama daga ke se wannan towel bakida kunya ne ko bakisan bakida mara ba da tsirarara ba" kallonshi tayi batace k'alaba taci gaba da murza man shafawarta tamkar bada ita yake magana ba,k'wafa yayi ita kuwa tayi Murmushi,can kuma ta taso tazo kusa dashi ta sunkuya ta juya masa baya,sassauta towel d'inta tayi tace
"Yaa Abdul plss ka shafamun a baya yana mun k'aik'ayi" kamar yace baze yiba se kuma ya lak'uci man ya murza a hannunshi,taushin lallausan hannunshi sanda ya sauka a wuyanta tad'an b'ank'are bazatace ga abinda taji ba awannan yanayin,yanayine na musamman da bata taba tsintar kanta acikiba me wuyar fassara,hakan take awurin Abdul tunda yake beji skin me santsi da laushi irin na Elham ba,Shafa man yake yana lumshe ido yakuma kasa dena wa sanda taga ze rikitar da ita tace cikin wata murya "Yaa Abdul har yanzu?" Lum sassun ida nuwansa ya sauke akanta yace "sorry network news nake kalla hankalina yana can" Murmushi tamasa tace "Tom na gode" wata hatsa bibiyar rigar bacci ta saka me had'e da wandonta iya cinya zip ne ta gaban rigar se faman janshi takeyi ya sak'ale tamkar Zata fasa kuka tazo kusa dashi

"Yaa Abdul dan Allah ka rufe mun zip d'innan mana kaga fa se janshi nakeyi amma mak'ale" d'agowa yayi ya sauke idonshi daidai cikinta,flat tommy d'inta ya k'urawa ido yace aranshi "wannan Yarinyar anyi yar duniya" Tasowa yayi tsaye ya janyota ya manna jikinsu tamkar ze maidata ciki sannan ya d'an matsa kad'an ya kamo zip d'inta a maimakon ya ja zip d'in seya cura hannunshi cikin rigar ya shafi tommy d'in ta murya k'asa k'asa yace "Hafsat wai nikam yaushe rabonki da saka abinci a cikinnan,jifa yanda ya lafe" hannunta takai saman Nasa dake kan cikinta take ta k'ara masa wani shock ya D'auke numfashi tace "Yaa Abdul meye haka? Dan Allah ka dena banaso" idonshi da suka sauya launi sabida azaba ya sauke mata yace "Menayi kuma?" Shagwabe wa tayi "Dan annabi nidai ka rufe mun zip d'in yunwa nakeji" dakyar ya iya rufe zip d'in,a wahalce ya koma ya zauna,juyawa tayi tana dariyar mugunta a ranta tace "Indai ina duniya kuma muna tare seka duk'awa me gadi da ahalinsa wlhy" Har takai kofar fita zuwa parlor dake d'akin ta dawo

"Yaa Abdul I'm hungry fa" k'ura mata ido yayi yace "Nasani yoghurt zakice kina wanka na saka an kawo miki" D'an lumshe ido tayi tace "But yau har da gasasshiyar kaza irin me d'awafi d'innan zanci plss,wasu lokutan idan akayi wa Baba megadi albashi yakan siyo mana" k'irjinshi seda ya doka jin abinda tace sarai ya sani dashi takeyi yace "Shirya mu taka anan bayan hotel nasan ana saidawa" da sauri ta wani daka tsalla tace "Yauwa bara na saka hijab kin na" Murmushi yayi yafara tariyo tsallen datayi yanda mazaunan ta ke girgiza san ransu,Shifa harga Allah ya kusa ajiye zancen Khamis gefe, idanma asiri suka masa aiba laipi bane danya kusanci matarshi kumama koda zasu rabu ai Gara yasan ya Mora,beside kyautuwa ma yayi a karya taba sakin matarshi,tunda ai zab:in momy ce,da wannan tunane tunanen har tace "Yar megadi na jiran Sarki me jiran gado,nafa kimtsa" beji dad'in maganar taba amma seya basar ya Mik'e kawai ya zura jallabiya rsa ya ce "muje" haka suka jeera suna tafiya ba mewa wani magana acikinsu,suna karya kwanar layin ya rik'e hannunta,kallon shi tayi batace komai ba,acan suka siyo suka k'aro juice suka juyo,har suka iso ba wanda ke magana,anan suka bace tare suka cin ye kazar tatas,mikewa tayi ta wanke baki ta dawo ta haye gadon ta kwanta abinta cikin nutsuwa bacci barawo shine ya sungumeta suka ware..... Ba ita ta farkaba se Wuraren karfe biyu na dare dama tana tsammanin zuwan period nata,aikam ciwon mara me tsanani ne ya tasheta,a razane ta tashi sai kuka,se Innah take kira tana yarfe hannaye,a k'asa ya kwanta dama saman carpet acikin bacci yaji kukanta ya farka da sauri yazo ya dagata ya daurata akan cinyarsa
"Hafsat lapia menene ya sameki haka" tana kuka tace "Yaa Abdul na Shiga uku mtrl pain ke damuna mutuwa zanyi" tsoro yaji sosai ya rasa me ze mata,acikin rudu yace "Me ake baki Idan yana miki ciwo ne?" Kasa ansashi tayi tayita kuka se tambayoyi yake mata amma sa. Ta kasa amsashi sabida azaba,kan kace me wannan tafara amai me tsanani da gudu take zuwa toilet yin aman,a haka har kusan asuba dawowa tayi ta kwanta akan cinyarsa duk ya damu tanata kukan,hannu ya sanya yana d'an patting bayanta a hankali,da kad'an yaji shiru koda ya duba tayi bacci sosai ta bashi tausayi yalwataccen gashinta duk ya baje ya rufe mata fuska se gumi take had'awa hannu ya saka ya janye mata gashin a hankali ya sunkuya ya sumbaci goshinta yace "sorry my wife, u will soon be well" kasa d'agata yayi ya barta anan tana bacci nta har bakwai ta gota sannan ya lallab'a ya ajiyeta ya je sallah,kuma dawowa yayi kasan cewar flight nasu se dare ze tashi ya sanya ya shige cikin jikinta ya rungumeta sosai suka ci gaba da baccin Su,har cikin ransa yakejin wani dad'i jinshi ajikinta wanda ya kasa gane ko dad'in menene.

*kumun uzuri Kuyi hakuri da wannan ina busy ne*

Mom Nu'aiym ce.

Hafsat ElhamOnde histórias criam vida. Descubra agora