RB-47

6.3K 759 174
                                    

Na yi murmushin mamaki ganin irin karfin halin Jibril, lallai maza basa da kunya yanxu har yana da bakin da zai ce min wai sai idan zan rabo da dansa? Ni zai kalli tsabar idanuwana ya ce min haka?

“Ba zaki iya rabuwa da Noor ba, ni kuma ba zan iya rabuwa da ke ba, ba kuma zan daina neman ki yafe min ba”

“Zan iya shiga?”

Na tambaya ina kallon security da ya tare kofar, sai ya kalli security ya ce

“Bata hanya ta wuce matata ce”

Da sauri ya janye min ya bude min kofa, ni kuma na shiga ina murmushin jin ya kira ni da matarsa lallai iska na wahalar da mai kayan kara. Ina gaba yana bina ba dan na san inda dakunan suke ba daman can Inna ce ta kwatantamin, har na wuce dakin sai ya kira da sunan da be taba kirana ba har na dauka cewar ba da ni yake ba

“Mrs Makama”

Ganin ban waigo ba yasa ya kara da cewar

“A nan dakin yake”

Juyowa na yi na dawo na shiga kofar da ya bude min, a yanayin yadda dakin Noor yake sai ka rantse da Allah ba cikin asibiti ba ne, ya kawata masa dakin da teddys ga wani madaidaicin plasma dake lake gurin freezer din dakin. Noor na ganina ya yi saurin saukowa saman gado ya doso inda na ke sai muka rumgume juna.

“Momy miyasa baki zo ba jiya da wata jiya kamin jiya?”

Dariya na yi na shafa kansa.

“Tan ba ga Daddynka yana kula da kai ba?”

Ta da kai ya yi ya kalli Jibril.

“Momy da gaske shine Babana?”

“Ee mana ba ga kamaninka nan kana ganin a fuskarsa ba?”

“Amman Babana Faruk fa?”

Daukarsa na yi na dora saman hospital bed din sai nima na zauna, Jibril kuma ya zauna a kujerar da ke fuskantarmu, sai na kama hannayen Noor na ce

“Baba Faruk ya rike ka kamar dansa, saboda a lokacin Babanka baya nan ya yi tafiya zuwa gurin karatu wata kasar, kuma baya son ace maka baya nan shiyasa ya fadawa Baba Faruk cewar ya ce shine mahaifinka kamin ya dawo”

“Miyasa Inna ta mareki saboda shi?”

“Saboda na boye maka gaskiya tun farko ban fada maka ba sai yanzu, tana ganin kamar ba zaka fahimta ba”

“Miyasa kika ce Uncle dina ne sai kuma yanzu kika ce shine Babana kuma?”

Yanzu kan ban san mi zan kara ce masa ba kuma, jin na yi shiru ban amsa masa ba yasa ya kara aiko min da wata tambayar.

“Ko dai da Baba Faruk ya rasu sai wannan ya dawo?”

“Aa kamin na auri Faruk na fara auren Babanka sai kaddarar aure ta raba mu, ya tafi karatu wata kasar sai Faruk ya aureni kai kuma ya rika ka kamar dansa saboda yana so na kuma ya san kimata, amman ba shine asalin mahaifinka ba, wannan shine mahaifinka na gaskiya shiyasa ake kiranka da Muhammad Jibril ba Muhammad Faruk ba”

Ya yi shiru kamar mai tunani sai kuma ya yi murmushin da ya bayyana hakoransa.

“Momy na gane, yanzu Babana be rasu ba kenan?”

“Gashi a gabanka kana gani, kuma yana son ka sosai kai har ma ya fi ni son ka”

Na fada ina nuna masa Jibril

Murmushi Noor ya yi sosai ga dukan alamun yaji dadin haka, sai na rika shi ya sauka saman gadon ya nufi inda Jibril yake yana ta kallonsa.

“Kuma fuskarmu guda ko Momy?”

RAI BIYUWhere stories live. Discover now