11

1.9K 130 10
                                    

🌹🌹🌹
           *_DR. HABIBULLAH_*
                         🌹🌹🌹

_writin by_📚✍🏻
     *_🌹 Firstlady🌹_*

      *WATTPAD*
@Ameenafirstladyy

*_🌈Kainuwa writers Association_*

11

Motarsu na Parking afnan ta wuce batareda data jirasu ba, da kanshi ya zagayo ya ɓude mata motar.
Jiki a sanyaye Jiddah ta fito, Kabir yace "muje ciki" harya juya zai tafi yaga takasa daga ƙafa.
Ji takeyi sam batasan ƙarasawa ciki batayiwa mommy adalci ba data zabga mata karya.
Wani kallo Kabir yabi ta dashi na tsantsan soyayya sannan ya gyara tsaiwa yace "jiddah ko bakyasan zuwan ne na takura miki"?
Girgiza kai kawai tayi  batareda tace komai ba...

Habibullah kuwa da shigowar shi kenan fitowa yayi daga cikin lafiyayyar motarshi, rufewa yayi tareda juyowa dan shiga cikin hall din.
Dumm yaji kanshi tareda saurin cire siririn farin glass dinshi.
Tabbas jiddah ce tareda wani wanda baisan waye ba, hasken fitilar dake haskaka wajan ne yasa ya gane jiddan ce dai tsaye duk da kanta a kasa yake...

"Jiddah ki ɗago idanuwanki ki kalle ni kiyi min magana idan bakyasan zuwan ne saina mayar dake gida..."

A hankali ta ɗago kai ta sauke idanuwanta kan nashi, da sauri ta janye su tana kawar da kai dai² saukar idanuwanta cikin na Habibullah.
Lokaci guda gumi ya fara jika mata fuska nutsuwar ta fara kaucewa dan yadda taga ya ɗaure fuska yana jingine jikin motar shi amma idanshi na kansu...

Saida ya gama kallesu sannan a zafafe ya koma motarshi yaja ta da gudun tsiya kamar zai tashi sama..
Tana ganin tafiyar shi ta dawo da kanta wajan Kabir wanda yaketa faman magana tun ɗazu daya fahimci hankalin baya tareda ita.
"Pls Kabir ka mayar dani gida yanzu"
Da mamaki ya kalle ta "lafiya jiddah lokaci guda kin rude haka"
"Pls nidai muje ka mayar dani dan Allah" ta marairaice mai Murya.
Ganin hankalin ta ya tashi yasa Kabir yace ta shiga su tafi,,,, ba bata lokaci ta shige tana jin gabanta na faduwa...

Gudu sosai yake shararawa tuni kanshi ya fara ciwo dan baya daukar pressure sosai, lokaci zuwa lokaci yakan yi ajiyar zuciya tareda wani huci mai zafi.
Kai tsaye part ɗinsa ya wuce ya sakarwa kanshi shower, ya daɗe sannan ya fito.
Saman bed ya faɗa tareda rintse ido yanajin wani zafi a cikinsu musamman idan ya tuna fuskar saurayin dake dauke da murmushi...

Kabir har gida ya kawo jiddah motar na tsawa ta fice bayan tayi masa godiya, jikinta sai tsima yakeyi tana buga gate din mai Gadi ya buɗe.
Ko juyowa batayi ba ta shige sannan Kabir ya tayar da motar shi ya bar wajan zuwa dinner...

Tana shiga ɗakinta ta wuce, wanka tayi sannan ta kwanta hawaye na zubo mata "meyasa nayiwa su mommy karya gashi nan najawa kaina yaya Habib ya ganni" ta faɗa hawayen na sake zuba..

Mommy da batayi bacci ba tayi mamakin jin dawowar jiddah tunda taji bude dakinta da sauri mommyn ta fito dan jin ko lafiya  ta dawo.

Jiddah na kwance taji bude dakinta, a firgice ta tashi ganin mommy ce yasa da gudu ta taso ta faɗa jikinta.
"Lafiya jiddah meya faru meya dawo dake yanzu".

"Mommy Dan Allah kiyi hakuri nayi kuskure"
Cikeda mamaki mommy tace "fadamin meya faru".?
Tana kuka ta fadawa mommy gaskiya sannan ta faɗa mata ganin da Habib yayi Mata.

Murmushi mommy tayi sannan tace "kinyi kuskure jiddah meyasa kika yimin karya, dakin fadi gaskiya ma da kaina xansa Hibban ya kaiki ki bari kwanta yanzu bari nake gun Habib ɗin" mommy tace tana kwantar da ita..

A kwance ta samu Habib idanuwan shi a rufe jin alamun shigowar Mutum baisa ya buɗe ido ba.
Zama mommy tayi gefensa sannan ta kamo hannunsa cikin nata.
"Habib" ta kira sunanshi a hankali..

DR. HABIBULLAHUnde poveștirile trăiesc. Descoperă acum