*HASKE WRITERS ASSO....💡*
💞 *ZAINUL ABIDEEN💞*
*SLIMZY✍🏼*
*Wattpad@slimzy33**5*
Kusan a tare suka shigo da Mai martaba da gimbiya bilkisu dukkansu a rude suke ganin yadda yake jijjiga ga idanuwansa da suka canja kala baka ganin bakin sai farin,cikin kuka gimbiya ta dubi Mai martaba Wanda ke tsaye tamkar an dasashi Yana kallon zainul gwanin tausayi,
"Ranka ya dade kayi shiru kayi umarni da mudaukesa mukaisa asibiti Mana ka duba kaga yadda yaron Nan yakeyi banaso in rasa d'ana shikadai gareni"cikin kuka take maganar,
Janyota jikinsa yayi ganin Haka yasa fadawan sukai saurin barin dakin yana bubbuga bayanta "haba bilkisu ya kamata kisawa zuciyarki hakuri da dangana Akan ciwon zainul tunda ba yanzun ya fara ba ba sabon Abu bane a wajenki Dan haka kiyi Masa addua kidaina wanan kukan Bari in dauko maganinsa Wanda doctor dinshi yabamu Akan dik lokacin da ciwon ya tashi abashi zai samu bacci"fuskarta jike da hawaye ta dago ta dubesa sai ta zare jikinta daga NASA ya juya ya fice ta tsaya gaban gadon zainul Tana kallonsa tausayinsa na Kara Shiga jikinta....Tana Nan tsaye Mai martaba ya shigo hannunsa rike da magani da cokali,da kansa ya sa maganin a cokali ya dama ya zo gaban gadon ya janyosa jikinsa da kyau saboda yadda yayi nauyi ya samu ya zuba masa a bakinsa dikda ba duka ya Shiga bakinba,
Yana Nan rungume dashi mahaifiyarsa na tsaye tana kallonsa kusan minti goma Sha biyar idanuwansa suka rufe alamar bacci ya daukesa....
*********
"Ummaty bazaki tsaya kici abinci ba?ki karya haka xaki fita da sassafen Nan?""Innah bazan iya cin komiba sai naje Naga halin da Yaya zainul yake ciki saboda inaji a jikina akwai abinda ya sameshi".....shiru innah tayi tana bin ta da kallo Sanan ta sauke ajiyar zuciya "to shikenan Allah ya tsare"
"Ameen innah"ta juya ta fita sauri sauri sanye da dogon hijabinta,....girgiza Kai innah tayi ikon Allah kenan Allah me hada jinin bayinsa batare da ya shawarcesu ba inbadan haduwar jini ba Ina ummaty Ina zainul abideen Dan sarki?...
********
Zaune take a gefen gadonsa ta zabga tagumi idanuwanta kirr akansa dik motsinsa akan idonta yakeyi yadda yake sauke numfashi a wahale kadai abin tausayi ne,....Tana Nan zaune taga Yana motsawa alamar kamar zai tashi,gudun kada ya Kara tashi da ciwon yasata saurin mikewa Tana tofa Masa ayatul kursiyyu da amanar rasulu kusan minti biyar sanan taga a hankali Yana bude idanuwansa tamkar Wanda gari ya wayewa ,idanuwansa sunyi jajir kamar ba idanuwansa masu fari Tass kamar Madara ba,...cike da tausayawa murya na rawa tace "sannu ya zainul"...kallo ya bita dashi batare da yace komiba jimm kadan taga Yana alamar son yayi magana ta Mike tsaye da sauri ta sa kunnenta daidai bakinsa Taji Yana ambatar ruwa...Da sauri ta juya side din gadonsa ta dauko gorar ruwansa ta zuba a glass cup har ta juya zatayi wajensa ta tsaya tsaye ta juya baya ta Shiga tofa Masa addua cikin ruwan sanan ta juya ta bashi a hankali yake amsa dikda yadda rabi ke zubewa,
"Umm.maty inaso intashi"shine abinda yace Mata bakinsa na hardewa,sanin bazata iya dagasa yadda ya Dace ba yasa ta fice da sauri zuwa parlor...
"Ya zainul ne yakeda bukatar tashi,shine nace ko zaku taimaka kuzo kusashi a wheelchair dinsa"
Wani mugun kallo dukkansu suke bin ummaty dashi Wanda yasata Tasha jinin jikinta,"ke kinma samu dama dayawa wallahi ki dubeki fa?kece zakizo kice muyi abu muyi?ko bamusan aikinmu bane malama?kinfimu sonshi ne?"ta girgiza Kai da sauri,
"To shisshigin na meye ne kin like kece ke jinya uwar iyayi shegen iyayi kamar wata uwar Mata ke ga me jinya kin kwaso kafa kice muzo muyi Abu kece ma ke bamu umarni to Baki isaba Yar talakawace ubanki ba kowa bane a gidan Nan sai sarkin Doki,ai da kin dorasa a wheelchair din tasa tunda kece ke jinyar,Ashe dai munada amfani"Tass suka karewa ummaty tanadi itadai Tana Nan tsaye kamar an dasata takasa cewa komi Tana sauraren irin cin fuskar da fadawa ma keyi Mata suda bakowa ba a gidan,..juyawa tayi kawai batare da tace musu komiba suka bi bayanta...
*********
"Ammiey na Shiga dakin ya zainul nasameshi kwance idonsa a bude,Amma ummaty Tana zaune Tana hawaye ammiey kukan me takeyi?"Shafa kanta tayi "afee ba kuka takeyi ba kila wani Abu ne ya shigar Mata Ido Amma me zaisa ummaty kuka?...Kinga ya kamata asama Miki lesson teacher saboda jarabawar Shiga senior section da zakiyi Koh?diyata ummul kairi ta girma"...take ta kauda maganar gudun kada afee ta cigaba da watso Mata tambaya,
"Jeki wajen anty fiyya ko Aysha kice nace Ina kiran daya daga cikinsu kinji?"...jiki Babu kwari Afee ta Mike Tana takawa a hankali ta fice a dakin ganin Haka yasa gimbiya mikewa ta nufi sashen zainul abideen taga meke faruwa...
*********
Ransa ba karamin baci yayiba da kalaman da wanan Yar rainin hankalin matar take jifansa dashi,lallai ma ta Gama Raina Masa wayau,kallonta yakeyi wanan karon Ido cikin Ido "gaskiya kin kaini makura a wanan tafiyar abinda kike Shirin aikatawa fa bazan iyashiba bazanyi ba wallahi saidai ki nemi wani yayi Miki shi Dan wanan aikin yanada matukar wahalar gaske"Murmushi tayi "meye aikin wahala a ciki?ai ka Gama komi sarkin dawaki wanan karashene ya rage kawai kayi shikenan kaga na cika burina sai sakamakonka Mai tsoka"
Takaici ne ya Kara lullubesa yadda take magana a gadarance Tana nuna shi kwadayayye ne shiyasa ya biye Mata suke wannan mummunan aikin kenan "wani sakamakon zan jira?Banda Wanda idan asirina ya tonu sarki zaisa a tsireni?karshenta kiyi amfani da makircin Mata ke ki kubuta ni in kwana ciki,Dan Haka bazan tabayin abinda kikesoba yanzun dai"
"Idan bakayi abinda nakeso ba to wallahi zanyi amfani da ummaty burina ya cika....kafi kowa sanin yadda nake akan abinda nakeso na kudira a Raina bani da sauran sukuni sai Naga na sameshi Dan Haka zanyi amfani da yarka wajen cikar burina,ko Kuma inyi sanadiyyar tarwatsa mata dik wani farin ciki na rayuwa...ni zanyi sanadiyyar da hanyar gidan Mai martaba ma idan ance tabi bazatabi ba,Dan Haka na baka Nan da zuwa gobe kaje kayi shawara....."
Gumi ne kawai ke karyo Masa ta ko Ina,ta wani fannin Kuma zuciyarsa keyi masa lugude tamkar zata fasa kirjinsa ta fito....babban tashin hankalinsa be wuce yarsa da takeso ta sa a bala'i ba shin menene Shirin wannan shedaniyar matar Akan yarsa?... innalillahi wa Inna ilaihi rajiun...bakinsa ke ambato jikinsa na tsananin rawa.....
*SLIMZY 😍*

YOU ARE READING
ZAINUL ABIDEEN
SpiritualBanida wani burin daya wuce Inga gawar zainul abideen akwance babban kudirina a duniya shine in bude idona Inga zainul abideen akwance baya numfashi inhar be mutuba kuwa bazan taba daina bibiyarsaba har saina tabbatar da na maidashi ga Rai babu amfa...