💫 _*EROTIC IDEAS*_ 💫
✍️ M SHAKUR
EPISODE 7️⃣
Yay maganan yana buga gaban mota aharzuke ganin yanda ranshi yay masifaffen baci yasa Abdul yay shiru bai kara cemai komiba harya kaishi wani nearby hospital akai treating wuyan yabiya kudin komi sanan suka dawo suka shiga motar yatada motar suka tafi, sundanyi nisa da tafiya sanan Abdul ya gangara gefen hanya yay parking tareda kashe motan yana kallon yanda Bash ya lumshe ido yau shiru, hannunshi yadaura kan kafadarshi ya matse sanan anatse yafara magana yace "look here Bash, bawai ina kokarin tauye maka hakki bane ko wani abuba, but I want you to think twice akan zancen dakake na rabuwa da Asiya aurenku yazo karshe, kunada 3 children kananun yara tare for that matter, kana ganin akwai wacce zaka auro aduniyan nan dazata kulanmaka da yaran nan tsakani da Allah kaman ita? See uwa uwace fa koma yaya take, just calm down think this through and fine the best solution, am your friend and I love you, I will always want the best for you, and bansan those little kids rayuwan su ya wulakance kaji, uhm Bash" bude idanu Bash yayi dasukai jajir ya kalleshi baki yabude zaiyi magana sai kawai yaji wani abu ya tokaremai wuya baisan ya akayiba saiga hawaye kawai chaaa sunhau zubowa yakai bayan hannunshi yana gogewa, Abdul baice mai komiba sai tapping shoulder dinshi kawai dayakeyi alamun yayi shiru is okay, almost 5min yadauka yana kukan mara sauta sanan yasamu da kyar ya tsaida hawayen, handky Abdul ya mikamai karba yayi ya goge fuskarshi tass sanan murya chan kasa datai rauni, dake cike da kunci dakuma damuwa sosai yace "zan kara aure Abdul" gyadamai kai Abdul yayi cikeda goyan baya, yacigaba. "banson nacigaba da rayuwa ahaka bakin cikin Asiya na turani inama Allah sabo, gwara na kara aure na auro wacce kesona sanan tasan darajata da amfanina, as for her nafasa sakinta for the sake of su Hydar but bayan su da wlh yausaina kadata gidan su" ahankali Abdul yace "kanada wacce zaka aura?" gyadamai kai yayi yace "inada shi" "then is settled cikin week dinan zamuje muga iyayenta kaikuma kafara gyara dayan side din gidanka anan zaka sata" gyadamai kai yayi sanan suka tada motar.
Parking sukayi suka fito sukai flat din, yaranshi yagani afalo suna tsalle tsalle suna kallon carton sun dawo daga islamiyya suna ganinshi suka ruga da gudu "Dady Oyoyo" dukansu yayi tareda sakin murmushi daidai Matar Abdul itama tafito daga kitchen din data shiga ta gyara Abdul na ganinta yace "kiramin Asiya" dan jim tayi ta tsaya tana kallonshi hakan yasa shima Bash yadago ya kalleta tabe baki yayi dan yasan miye zatace, Abdul yace "me kika tsaya kina kallona"? Ahankali tace "I tried my best to stop her but taki ta tafi gidansu" juyowa Abdul yayi ya kalli Bash daya daukekai kaman baimasan sunayi ba, tashi Bash yayi yace "common children let's go to grandma's House" sunajin grandma sukahau ihu, yajuyo ya kalli Abdul dake kallonshi yace "tashi mutafi" tashi kawai Abdul yayi baicemai komiba suka fice daga dakin gabadaya bayan ya kwaso kayan matan Manzil daya sayo mata ya sakasu a both din motarshi, su Abdul suka shige motarsu shikuma ya shige nashi da yaran suka fice sai gidan Mahaifiyar shi dake tawajajen gwamna Road, baima karasa parking ba Hydar yabude kofa har yana neman fadi babu yanda zaiyi haka ya kashe motar duk suka fice sanan yakarasa yay parking sanan yafito yay cikin gidan, sallama yayi ya shiga falo Mahaifiyarshi yagani zaune kan carpet akasa yaran sunyi dama sama ajikinta suna mata surutai tana biye musu, ganin danta Bashir ya shigo yasami waje daya yazauna yana kallonsu yasa tabishi da kallo dan tuni ta karanci damuwa tattare dashi barin ma yanda idanunshi sukayi, bandejin data gani a wuyanshi yasa da sauri tasaki yaran tana kwalama yar aikinta kira. "wai ina Indomie da yaran nan sukace suna sone shafa, nagadai minti daya yay yawa agama dafa Indomie" daga kitchen yarinyar tace "yanzun nan zan gama Hajiya" remote ta dauka tasaka musu carton sanan tace "ku dagani kuga ina zuwa bari nai magana da baban ku" dagasu tayi ta tashi sanan ta kalli Bashir tace "meet me in my room" tai gaba, ahankali yatashi daga kan kujeran yawuce ciki, bude kofar dakinta yayi ahankali da sallama ya shiga tsaye ya ganta tana binshi da kallo tundaga sama har kasa kafin ta nunamai kan gadonta da hannu babu alamun wasa kan fuskanta tace "zauna anan" karasawa yayi ya zauna abakin gadon ahankali gabanshi na faduwa, karasowa gabanshi tayi takai hannu kan wuyanshi yatsine fuska yayi yace "ahhh" dan yaji zafi yace "Mum mehaka stop" ko kallonshi batayiba saida ta warware bandage din tas sanan ta dagakai ta kallai tace "who did this to you"? Shiru yayi yana kallonta yakasa magana dan Mum nada fada kuma bata wasa da yaranta, barin ma shi bala'in sonshi take bana wasaba, yasan yagayamata she can do the unthinkable, dakamai tsawa tayi tace "I said wayaji maka ciwo haka awuya Bashir bakajini bane"! Ahankali yace "ahhh Mum is no big deal, um buge....w......" "wlh kamin karya anan saina gaura maka mari, give me an answer waya jimaka ciwo haka awuya" ganin yanda ta harzuka take tafarfasa yasa yakama hannunta ahankali yace "Mum please calm down bawani ciwo bane" ihu tamai aka tace "don't tell me to calm down, tayaya zan calming down ana kokarin kashemin d'a, jibi wuyanka inda an samu any vein dinka na wuya haka zakai bleeding out and die wa akama asara ni, waya ji maka ciwo haka awuya?" shiru yayi yakasa amsata no matter meke faruwa tsakanin shi da Asiya baison Mum ta sani dan mahaifiyar shi mace ce da ta tsani wanda ya tsani y'ay'anta, takanyi fada da uban kowa kan yaranta batada kawaici kan yaranta. "Asiya ce tamaka haka ko"? Jin ta ambato sunan Asiya yasa da sauri ya kalleta yace "Mum no ba ita bace" bata sake cemai komiba tajuya tadau wayarta dake kan table tai dialing number yana ganin haka yatashi yace "Mum wakike kira"? Batare data kalleshi ba tace "mahaifiyar Asiya" da sauri yakai hannu ya fizge wayan tareda kwashewa yace "Mum please mena kiran Mamanta, we had an agreement, nima ai na daketa, please kiyakuri kinji" yay maganan idanunshi na ciccikowa da kwalla, nan hankalinta yakara tashi lallai Asiya ta cutar mata da da dayawa, Bashir ne harda kuka, rabon dataga kukan Bashir tun yana yaro dan namiji ne, ahankali tadawo kan gado ta zauna tareda nunamai gefenta zama yayi shima, cikeda muryan lallashi tace "banson kana boyemin matsalar ka, tell me everything Bashir, I am here to listen and to guide you, wats happening in your home"? Kaman bazai fada mataba saikuma yafadi mata komi har karin auren dayake so yayi, na'am tayi tace "badai ta tafi gidansu ba wlh bazakaje ba, kuma saika kara aure tai kadan ta gayamaka abinda zakayi da wanda bazakayiba, itadin wacece tasan waye d'ana sabida taga kana sonta, kaje gida ka kwasomin kayan yaran nan tass, suna gidana harka karo aure, tunda bazata iya kuladasu ba ni inason jikokina zan iya, zan dauko musu nani gobe, daganan zasu dinga zuwa makaranta inga tazo gidan nan tazo ta gansu naga, zan kira Baffan ka jibi saisuje tambayo maka auren Aya, don't worry okay, I got u, je dakinka kai wanka zansa akawo maka abinci yanzu kaci saika tafi kwasomin kayansu" gyadamata kai yayi yatashi tabi bayanshi da kallo gabaki daya ya rame ya lalace yay shegen duhu kaman ba danta ba, mesa mata ke iskanci insuka lura mazajen su na sonsu newai.
![](https://img.wattpad.com/cover/253223473-288-k376022.jpg)