3. Meh wannan?

2.4K 155 41
                                        

Mufeeda and Aisha

Oops! This image does not follow our content guidelines. To continue publishing, please remove it or upload a different image.

Mufeeda and Aisha

Fahad and Elmansoor

Oops! This image does not follow our content guidelines. To continue publishing, please remove it or upload a different image.

Fahad and Elmansoor

Asma'u na jin mutuwar aminiyarta na'kuda ya taso mata, bayan gajeruwar nak'uda ta haifo nata yarinyar kyakkyawa gwanin sha'awa.

Mutuwar Amina da sati d'aya aka sa wa yaran suna, duk da ba taron suna akayi ba saboda rasuwar. Yarinyar marigayiya Amina an mayar da sunanta wato Amina amma suna kiranta da Mufeeda, yarinyar Asma'u kuma Aisha aka sa mata, sunan mahaifiyar Abdullahi, ba a b'oye mata suna ba dan mai sunan tace batason a k'ira takwararta da sunan turawa, a cewarta canja suna ba komai ke sawa ba sai b'atar da sunan yara.

Asma'u ce ta shayar dasu dukka, tana matuk'ar nuna kulawarta garesu musamman ga Mufeeda, haka kawai watarana zata ajiyesu tana kallo tana hawaye wai Mufeeda na tuna mata marigayiya.

Bayan shekaru biyu bayan an yayesu mahaifin Mufeeda ya nemi a dawo masa da ita, basu yi jayayya ba suka tattara suka kaita gidan mahaifinta, kamar tana sane da za'a rabata da da uwar goyonta ana shiga da ita gidan ta fara tsala ihu, bata tsagaita kukan ba har Abdullahi da matarsa suka bar gidan hawaye taf idanun Asma'u.

Dak'yar ranar tasha madarar da amaryar babanta ta had'a mata, har dare tak'i bacci sai zabga kuka take, wasa wasa kwana uku Mufeeda tak'i daina kuka, tun ana cewa bata saba bane har aka gaji aka d'auke ta aka mayar da ita gidan goyonta, sanadiyyyar zamanta wurin iyayen Aisha kenan.

Suna shekaru 9 mahaifin Abdullahi ya rasu, a lokacin Abdullahi da iyalansa sun koma Abuja da zama. Abdullahi yaji rasuwar mahaifinsa, kuka yayi ta yi kamar k'aramin yaro, da aka gama sadaka ya nemi ya tafi da mahaifiyarsa tace bazata bar gidan mijinta ba, ita ma anan mutuwa zai d'auketa kaman yanda ya d'auki mijinta.

Ba dan yaso ba ya barta a can Damaturu. Yanzu da suke shekaru 17 suna ss2, Aisha na da k'anne uku, biyu maza autarsu mace, ko wane hutu a Damaturu suke yinsa, ko a gidansu Mufeeda ko gun kaka tsohuwa.

Hutun 1st term ss2 suka samu, tuni suka shiga shirin tafiya.
"Irin dariya haka? Meh kuka samo mana yau? Ko duk murnar tafiyar ne?"
Shigowar Mama kenan d'akinsu taji suna hira had'e da yin dariya, Aisha na tsaye gaban wardrobe tana ciro musu kayansu da zasu tafi dashi Mufeeda kuma na sawa a akwati.

SOYAYYA CEWhere stories live. Discover now