09. Kin daina kukan?

833 72 40
                                        

"Wayarta ma na kashe na d'auki naka, meh ya faru?" Yayi maganar yana sosa karan hancinsa.

"Yi hak'uri na k'ira ba lokacin da ya dace ba, in ka gama da ita muyi magana kawai". Fahad ne yayi maganar ta d'aya b'angaren yana k'ok'arin kashewa muryar Elmansoor ya dakatar dashi.

"Tsaya mana tunda na d'auka, kasan meh? Maganan Aisha ne, ni fa halinta ya fara damuna, anya tana sona kuwa?".

Shiru Fahad yayi dan kalaman bakinsa sun samu wani rami sun rufe kansu ciki. A asibiti yayi ta tambayarsa shin Aisha ta nemesa dan taji ya yake? Bai b'oye masa ba yace a'a, shi kansa Fahad yayi mamakin rashin nemansa da tayi duk da yasan bata da lambarsa, ba'a tab'a samun budurwar da Elmansoor yayi ba har sati basu yi waya ba bata k'ira Fahad ba sai akanta, da alamu hakan ya b'ata ran Elmansoor, hakan ya fara sa shi kokwanton soyayyar da take masa.

"Elmansoor haka kakeyi fa ita ma tayi maka? Kai kace kana son mace mai ra'ayi irin naka, ka samu kuma sai ka fara complain?"

K'aramin tsuka Elmansoor ya ja yana lumshe ido, zuciyarsa na masa zafi, bai san ya zai sa masa maganar ta yanda zai fahimta ba.

"Ka gane Fahad, yarinyar nan bata k'irana fa kamar sauran, in kaga ta k'irani toh wallahi da dalili, kuma yanzu nayi sati bamuyi magana ba bazata nemi layinka ta k'iraka ba? Kuma tana da layin Humaira, abun nata lafiya? Anya tana sona? Yanzu da na k'irata ma instead a tarbeni da magana mai dadi complain wai take min? Wai ban k'irata ba for a week? Toh in ban k'irata ba meh yakamata ta yi?"

Fahad daga d'aya b'angaren murmushi yake sakarwa ba tare da Elmansoor ya gane ba, irin matan da ya dace Elmansoor ya samu kenan tun farko baiyi dace ba, da sannu zai gane kurensa, da sannu zai fuskanci abunda kullum Fahad ke sanar dashi, Aisha ce kad'ai daidai shi, tafi dacewa dashi, ga dukkan alamu ta samu matsaguni cikin zuciyarsa.

"Kasan meh Elmansoor, abun nan guda d'aya ne, in kana son ka gane tana sonka ko bata sonka ka nuna mata so, in bata nuna maka kamar yanda ka nuna mata ba nan ne zaka yanke hukunci, amma yanzu watak'ila halinka yasa take d'aga maka k'afa, wata k'ila ta d'auka hakan kakeso shiyasa take maka..."

"Fahad" ya dakatar dashi muryarsa na nuni da gajiyar jin shawararsa, yasan bazai tab'a yi ba meh na fad'a masa?

"Su sauran 'yan matan haka sukayi? In tana sona ai irin nasu zatayi"

"Halinku yazo d'aya, ku canja juna"

"Sai anjima" yace a k'ufule tare da katse wayar.

Mintuna masu yawa tsakani sannan ya k'irata bayan ya gama bawa kansa baki.
"A kashe kuma? Haba Aisha, wannan yarinyar zata zautani, so take inyi ta binta kenan?"
Dafe goshinsa yayi yana mai sauk'e nunfashi.

~~~~~~~~

Kuka takeyi mai shiga rai, ji take kamar zuciyarta na iya tarwatsewa a kowani lokaci, kanta sarawa yakeyi amma ta gagara tsagaita kukan, so take a kowani hali ta yakice wannan murd'ad'en saurayin wai shi Elmansoor, bazata iya rayuwar nan ba, bazata iya d'aukan haka daga wurinsa ba, wato ita ya mayar sidechick? Lallai ya raina mata wayo.

Sim nata ta cire daga wayar dukka ta ajiye cikin jakar hannunta, alk'awari tayi bazata kunna ba bare ya samu daman k'iranta.

Sosai tayi k'ok'arin kawar da damuwarta, bugun duniya Mufeedah tayi amma tak'i sanar da ita yanda sukayi, kuma tak'i nuna damuwarta a fuska sai dai wayarta da ta kashe.

SOYAYYA CETempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang