6. Kokwanto

1K 121 51
                                        

NAGARTA WRITERS ASSOCIATION

SOYAYYA CE!

Alkalamin MaryamerhAbdul

Page 6

A cikin kwanakin nan Aisha ta karanci Elmansoor tsaf, tafi kyautata zaton yana daga cikin mutanen nan shiru-shiru, da wuya yayi mata doguwar magana ko da tambayarsa tayi, maganar soyayya kam tuni yayi fatali dashi, a ganinsa tunda ya fad'i kudurinsa kuma tana magana dashi ta aminta kenan.

Shirun ta da rashin damuwarta akan hakan ya k'ara sakewa da ita, a ganinsa hali yazo d'aya bai san karantarsa ake ba.

A hirar da tayi da Mufeeda ta sanar da ita abunda ta gano game dashi, kuma ta bata shawarar da ya dace, tunda tana jin sonshi meh zai hana ta gwada yin nata bajintar ko zai dawo yanda takeso?

~~~~~~~~

Sun gama hutu a Damaturu suna shirin komawa gida, mama da Abba sunzo sunyi sati d'aya tare zasu koma, kowa ya fito da jakarsa da kayan da zasu tafi dashi, kaka tsohuwa ta had'a musu tsaraba irin nasu na tsoffi irin su magarya, kurna, kuka, daddawa, busasshen kub'ewa da sauran kayan marmari da na miya.

Mufeedat ta 'dauki leda tana 'diba magarya kaka tsohuwa ta shigo d'akin.
"Ki fito da sauran kayan shine kika zo kika zauna ko?"

Kallon Mufeedah ta tsaya yi ganin d'iban mata magarya take.
"Lallai yarinyar nan, tsaraban nawa kike kwashewa? Ki juye min abuna kafin in sab'a miki".

Ganin bata da niyyar magana yasa ta cigaba da cewa "meh zakiyi dashi ne wai?".
Shagwab'e fuska Mufeeda tayi tana kallon kakar tata.
"Yau fa zan tafi amma kike min haka? Ci zanyi a mota, har kin manta yanda 'yar jikallenki take son magarya, tsufa dai yazo".

Washe-baki tayi tana mai gyara tsayuwarta a bakin k'ofar, "in ke zaki ci da sauk'i, na d'auka wani zaki baiwa, abinda na sayawa d'ana ki kaiwa wasu, ai da sai kin biyani".

D'auko wani ledan Mufeeda tayi tana bud'ewa
"Ai kin ma tuna min in d'ibarwa saurayina, shima son abin nan yakeyi sosai...".

Bata ida maganar ba Hajiya ta warce ledan, "wallahi baki isa ba, ba dai a wanda na sayawa 'dana ba, ki saya masa in kinason birgeshi ne, in kuma sai nawa yakeso yazo ya gaisheni da kayan dad'i nan zan fara yi masa tsaraba shima".

Sosai ta fashe da dariya ganin da gaskiya Hajiya ke maganar, shigowar Abba yasa ta tsagaita dan k'aramin aikin Hajiya ne ta fallasa ta wurinsa bayan ita tsokanarta take son yi, fita tayi daga d'akin ta basu wuri bayan ta d'auki sauran kayan.

~~~~~~

Abba da driver ne a gaba, sai mama da sauran yaran a tsakiya, Mufeeda da Aisha kuma a baya, irin motar nan ne mai gida uku, dan tafiya irin wannan musamman aka sayo.

Suna cikin tafiya Elmansoor ya fad'o mata a rai, rabonta dashi tun shekaran jiya bai nemeta ba ita ma haka, wayarta ta d'auko dan tura masa sak'o, bazata yi zuciya tun wuri ba, zata bashi lokaci ta ga yanayin yanda zasu kaya.

~~~~~~~

Cikin bacci yaji wayarsa alamar message ya shigo, jiki a mace ya lalubo wayar ba tare da ya bud'e idanunsa ba.

A hankali ya bud'e idon dan duba wanda yayi masa sak'o da safiyar lahadi bayan ansan ranar hutu ne ga kowani ma'aikaci. Aisha ya gani rubuce saman screen nasa kamar yanda yayi saving layinta.

Bud'ewa yayi ya karanta:-
"on my way, jiya bamuyi magana ba ban samu daman sanar dakai zan dawo yau ba, nayi kewar hira da kai... i love you''.

Murmushi ne ya mamaye fuskarsa dan yaji dad'in kalamanta, bazai ce yayi kewarta ba amma yana jin wani sashe na zuciyarsa na kwad'aitar dashi son magana da ita, basu fahimci juna ba, bai san komai game da ita ba, ya bar wannan har bayan dawowanta gari yaje har gida su gana, hakan kamar yafi dacewa ko?

Ajiye wayar yayi ba tare da yayi mata reply ba ya lumshe idanunsa zuciyarsa fes yana mai jin farinciki a ransa, kalamanta ya dad'ad'a masa rai, bata tab'a yi masa hakan ba, tayi kewarsa tace, har ma da tana sonsa, tunda yake da ita bata tab'a rubuta masa hakan ba.

Kamar bazai mayar mata da amsa ba ya tashi ya shiga kewaye yayi brush ya wanke fuskarsa ya dawo ya zauna dan ya amsa ta, meh zai ce mata? I love you too? Ko kawai yayi mata addu'ar isowa lafiya? Numfashi ya ja ya sauk'e sannan ya fara rubutu.

"Nagode A'ish habibty, Allah ya kiyaye hanya..."

Da hanzari ya danna wurin goge rubutu yana magana a fili "What? Ni nake rubuta wannan abun? Habibty?" Dariya ne ya kufce masa yana kallon inda ya rubuta A'ish habibty, shi yake tsarawa mace kalamai haka? meh zata 'dauke shi in ya tura mata wannan sak'on? Da girma ya zube kuwa.

Dukka rubutun ya goge ya rubuta sabo sannan ya tura mata, sai da ya tabbatar ya isa gare ta sannan ya mik'e ya shiga wanka dan lokacin k'arfe 11 ya goce.

~~~~~~~~

Aisha kam she is stuck in the car, tun tana jiran amsarsa har ta fidda rai ta tsuke baki tana kallon Mufeedah da ke game a wayanta, bata da damuwan komai, tunda ta rabu da saurayinta Shaheed bata sake kula wani ba, ta soshi kamar ranta, daga k'arshe iyayensa suka bashi cousin d'insa, hakan yayi sanadiyyar rabuwarsu.

Hira ta fara yi mata dan kad'aici da takaicin Elmansoor na neman b'ata mata ranarta, ta cire tsammanin ganin sak'onsa taji k'arar wayarta. Da farincikinta ta bud'e ganin Elmansoor ne ya dawo mata da martani.

Idanunta ta kifta dan sak'onsa da ya shigo ko layi d'aya bai kai ba, rubuce yake kamar haka "Safe, nima haka...
Elmansoor!"

Baki bud'e take kallon wayar tana mamaita karanta sak'on, tsaki ne ya kufce mata bata san lokacin da tayi ba, Mama tuni ta juyo tana kallonta.

"Meh hakan? Bance banson tsakin nan naki ba? Yaushe zaki ji magana wai?". Cikin fad'a tayi mata maganar.

Aisha bakinta ta rufe da hannunta bata iya cewa komai ba, dan dama kullum fad'ansu da Mama kenan tsaki, Mufeeda kuma dariya ke cinta ta k'asa tana toshe baki, taso gano dalilin tsakin nata dan taji lokacin da sak'o ya shigo wayar, sai da Mama ta juya sannan ta nuna mata message d'in.

"Ki ga mutumin nan, duba message d'ina ki duba nasa. Nima haka? Son ne shima haka ko missing d'in da nace nayi?"

K'asa-k'asa take maganar dan kada Mama taji, bata jira amsar Mufeedah ba ta shiga whatsapp ta nuna mata hirarsu, kusan rabin hirar tambayoyin Aisha ne da take masa, amsarsa bai wuce eh, a'a ba, sai kuma similey na dariya ko blush. Taya zata iya rayuwa da mutum irinsa? Ta fara kokwanton son da yace yana mata.

********

Comment a kowani layi
Danna tauraron nan
Kuyi sharing labarin zuwa ga masoya da abokan arziki.

Nagode
MaryamerhAbdul

SOYAYYA CEOnde histórias criam vida. Descubra agora