BABI NA ASHIRIN

1.8K 291 18
                                    

MAKIRCI KO ASIRI

Rubutawa
Yar_ficika

®️NWA
Wattpad yar_ficika

BABI NA ASHIRIN

The beautiful memories of the times we've spent together make me smile, only until the moment when they eventually remind me that you're no longer here. I miss you Maama,💔😭 I dedicated this page to my one nd only, my lovely, my everything Mom♥️ may Allah bring peace in ur grave nd make aljannah firdausi ur permanent home🙏🏼😭 Maama ur Auta loves you so much, l'll never stop crying for loosing you😭😭 I love you Hajiya Maama ♥️

Yana fita ta d'ora kanta jikin Haneef tana kuka, gaba d'aya yaran kuka sukeyi, babu mai lallashin wani, tsaye yake kamar gunki ya kasa motsi zuciyanshi wani irin zafi yake mashi, duk da yasan yanzu yaran basu gabanshi, amma ya ji mutuwa Haneef saboda yaron ya shiga ranshi sosai..
Ahmad ne ya dawo da sallama yana gaba doctor na biye dashi, gaban gadon doctor ya k'araso gwaje gwaje yayi yakai minti goma yana gwaje gwaje, daga k'arshe da ya d'ago yace
"Sai dai muyi hak'uri Allah ya karb'i abunshi."
Kuka ne ya kufce mata, ta k'arasa wajen gadon Haneef da gudu tana kuka,
"Haneef katashi dan Allah ka tashi munasanka ni dasu Adda dan Allah Haneef ka tashi"
Babu wanda baiyi kuka ba, harta likitan saida yayi kwalla.
Haneefa ce ta k'arasa wajenta ta kamo ta tace
"Ammi kiyi hak'uri Haneef ya tafi ya barmu adu'a zamu dinga mashi amma kinsan bazai dawo ba da ana mutuwa a dawo da babu wanda zai bari nashi ya mutu bai maidoshi ba, ki godema Allah ya ronki ya rasu yana neman yafiyarki dama gashi yaro bai balaga ba kiyi ta wakkali Allah bazai barki haka ba sai kinga sakamakonki nan gaba, kima gode ma Allah ya rasu ya huta da wannan rayuwan da muke ciki..."
Sakin baki likita yayi yana kallonta "dama akwai yara masu irin wannan baiwar? Lallai kowa da baiwar da Allah ya mashi.." ciki zuciya yake wannan tunani...
"Likita muje office kabamu bill d'inmu mutafi dashi dan yau za'a mashi sutura gobe in shaa Allah akaishi gidanshi.."
Ahmad ne ke fad'ama likita haka, fita likita yayi Ahmad ya bishi baya dan yayi clearing komai, su tafi gida da gawan Haneef. Saida Ahmad ya gama da asibiti ya biya bill d'in da aka mashi yadawo d'akin inda ya tarda wasu nurse sun shirya Haneef d'aukarshi akayi aka sashi mota, suka nufi gida......

***********
Abinda ya faru, Ahmad na fita daga cikin gidan, Imran ya biyoshi baya, harya tada mota zai tafi, yaji an bud'e gaban mota an shiga, bai tanka mashi ba ya ja mota yabar haraban gidan, saida ya tabbatar da ya hau titi, ya juyo ya kalli Imran, kauda kanshi yayi yace
" Ina zan kaika? Danni asibiti zan koma"
"Nima asibitin zani, inasan in ganshi inga halin da yake ciki.."
Juyowa Ahmad yayi ya kalleshi daga nan ya kauda kanshi bai k'ara mashi magana ba har suka iso asibiti......

************
Daidai bakin gate d'in gidan Imran, Ahmad yayi horn maigadi ya lek'o ganin motan Ahmad ne yasa ya koma da sauri ya bud'e masu gate, shiga yayi cikin gidan ya samu wuri yayi parking, suna fitowa mai gadi na k'arasowa
"Hajiya ya jikin Haneef? Ko an sallameshi ne?"
Ya fad'a yana kallon Ramlah, gaba tayi dan bata iya bashi amsa...
Ahmad ne ya bashi amsa da
"Allah yayi ma Haneef rasuwa"
Tun kafin ya ida Baba maigadi ya fara salati yana sharan kwalla, gaba d'ayansu sukayi cikin gida banda Baba maigadi da aka bari tsaye yana hawaye....

Suna shiga Ramlah ta saka hannu ta amsheshi daga wajen Ahmad tayi d'akinta dashi, zaune suke parlour Ahmad da Imran sunyi jugum jugum, babu mai ma wani magana. Da karairaya ta fito parlour bako sallama ta samu wuri kusa da Imran ta zauna, hannunshi ta zare daga tagumi tace
"Baby kadawo kenan? Wai inama kaje?"
"Asibiti naje"
Ya bata amsa.
"Aww hakane fa ya mai jikin?"
D'agowa yayi jiki ba kwari yace
"Yarasu"
Tab'e baki tayi tace
"Allah ya jikan nusulmi"
Amsawa yayi da
"Ameen"
Duk abinda ya faru idon Ahmad na kasu wani mamakine ya rufe shi,
"Anya matar nan kuwa tasan Allah? Duk abinda yafaru ita ce sila amma yanzu kalli yanda ta nuna abun bai dameta ba, zanyi maganinki..."
Cikin zuciya yake maganarshi, tana d'agowa suka had'a ido da Ahmad, wata harara ya watsa mata sai da gabanta ya fad'i...

Tashi tayi tace
"Baby natafi in kwanta sai ka taho"
Tana fad'in haka ta juya ta nufi d'akinta, Imran na d'agowa idanuwansu suka had'u waje guda shida Ahmad, harara Ahmad ya wurga mashi..
"Katashi kaje d'akin Ramlah ku zauna da gawan, ni zan zauna nan"
"Bazan iya zuwa ni kad'ai ba please muje tare sai mu kwana da gawan ita idan yaso sai ta tafi d'aki da yaran.."
"Akanmi zamu rabata da d'anta sai dai kai ku zauna tare da ita" marairaice mashi yayi yace
"Ban iya zama da ita kusa dani"
"Why?"
"I hate her, na tsaneta na tsani na ganta kusa dani duk idan tazo kusa dani daurewa nakeyi, wallahi bazan iya zama kusa da ita ba har mu kwana zan iya mutuwa nima.." Galala Ahmad ya saki baki yana kallonshi, dan tabbas baccin yasan waye Imran da sai yace shaye shayen zamani yafara, amma wannan ko ba'a fad'a ba kasan bayin kanshi bane ba, saboda irin san da Imran ke ma Ramlah kowa yana mamaki amma yanzu yana fad'in ya tsaneta....
Banza Ahmad yayi dashi, kamar ba dashi yake magana ba, kwanciya yayi bisa kujeran da yake zaune yayi, shima Imran d'in kwanciya yayi, alamun bazaije d'akin Ramlah shi kad'ai ba....
Ganin da gaske yake Ahmad ya mik'e yace
"Muje"
Ba musu kuwa yabi bayanshi, da sallama suka shiga d'akin zaune take k'asa ta kunna karatun qur'ani, ta d'aura kan Mukhtar bisa ciyarta da alama yayi bacci, Haneefa na gefenta tayi tagumi...
"Ramlah kuje d'akinsu Haneefa kubarmu zamu kwana da gawan"
Ta bud'a baki zatayi magana yace
"Ah ah karki man gardama kiyi yanda nace baki ganin Mukhtar yayi bacci kuje can d'in mu muna nan.."
Ba yanda ta iya dole ta tashi ta d'auki Mukhtar taja hannun Haneefa sukabar d'akin.....

****
Tana shiga d'aki fad'awa tayi kan gado tana murna, wayarta ta jawo ta danna kira, har wayan ta tsinke ba'a d'auka ba, k'ara dailling number tayi, saida ta kusa tsinkewa kana aka d'auka.
"Hello Mufeedah lafiya kike kirana cikin dare haka?"
Murmushi tayi tace
"Kiyi hak'uri Lash Ban iya bari sai da safe ban maki albishir ba."
"Miyafaru? Ina jinki"
"Haneef ya rasu"
"Wane Haneef?"
"Yaron Ramlah mana."
"Miyafaru? Gayaman dan nasan koma miye kece sila."
Dariya tayi sosai tace
"Kamar kin sani." Nan ta kwashe komai ta gaya mata, shewa sukayi gaba d'aya,. "Gaskia Mufeedah baki da kyau"
Ajiyan zuciya tayi tace
"Ay dama nace ni zanyi komai da kaina, sai dai bashi naso ya mutu ba wannan marar kunyar yarinyar naso ta mutu, dan Haneef ya d'an shiga raina...
Dariya Lash tayi tace
"Itama bani kokonto zaki gama da ita soon." Dariya suka saka, haka suka cigaba da hira kamar wani abu bai faru ba daga k'arshe sukayi sallama kowa ya kwanta.....

9:00am
K'arfe tara daidai aka shirya Haneef dan kaishi gidanshi na gaskia. Fitowa akayi dashi za'a tafi dashi, tashi Ramlah tayi ta rik'e gawan tana kuka ganin haka yasa Haneefa kuka ita da Mukhtar duk wanda ke parlour babu wanda baiyi kuka ba, sai Mufeedah dake latse latsen waya.....
Dak'yar aka janye Ramlah daga jikin Haneef, tanaji tana gani aka wuce da Haneef makwancinshi na gaskia, ana fita dashi ta fad'i k'asa sumamma, da gudu mutane sukayi kanta, ruwa aka dinga yayyafa mata dakyar aka samu ta farfad'o. Tana farfad'owa ta had'a Haneefa da Mukhtar ta rungume tana kuka, babu wanda bai masu kuka ba, duk rashin imaninka sai kayi kuka......

Inama duk d'an team d'in Ramlah ta'aziyan rasuwan Haneef, nasan duk kuna team d'in Ramlah. To ni gaskia zan koma team din Mufeedah, lolzz wasa nake nima Ina nan team d'in Ramlah... Dan Allah karku manta kud'an danna tauraro nan na hannun hagunku, sai kuma ku shiga akwatin nan ku aje ra'ayoyinku, nagode Allah ya barni daku ni daku k'auna ce wadda bata da k'arshe idan babu ku babu feedoh, kusani Ina k'aunarku each nd every second♥️ I love y'all my hayatiees😘
#team MKA
#1love

MAKIRCI KO ASIRI Where stories live. Discover now