BABI NA TAKWAS

2.2K 195 14
                                    

MAKIRCI KO ASIRI
               
              Rubutawa
                     Yar_ficika

®NWA

Wattpad @yar_ficika
Blog
Phirdauceejeebo.blogspot.com

BABI NA TAKWAS

   Shiru Ramlah tayi dan tabbas tasan Haneefa gaskia take fad'a mata dole ta tashi tsaye da adu'a dan matar nan da alamun batazo da zaman lafiya ba, ita har mamakin Haneefa takeyi a iya shekarunta amma tasan ama wani abinda bai dace ba....
    Tana shiga d'aki tajawo waya ringing biyu aka d'auka
"Hello Lash kina ina?"
Banji mi akace ba,
"Ok kizo gidana yanzu ina san ganinki", tana fad'ar haka ta datse call d'in, tashi tayi ta dinga zurga zurga cikin d'akin
"Hmmm Ramlah zaki raina kanki dake da marar kunyar d'iyarkin nan zaku san wacece Mufeedah yar ruwan zafi baka tab'ani bama na k'ona ka bare ka tab'ani da nayi niyar in d'an barku amma naga d'iyarki tsaye take to dole zanyi maganinku da wuri sai na mai daku abun tausai a gari...
    Haka ta dinga zagaye d'aki tana sabbatu ita kadai..
                        *******
     Banko k'ofa tayi ta shigo ko sallama babu
"Lafiya Mufeedah?"
Sai a sannan ta juyo, murmushi tayi taja hannunta suka zauna bakin gado...
    "Ina jinki fad'aman ko hankalina ya kwanta"
Dafa kafad'arta tayi tace
"Akwai matsala"
"Matsala?"
"Eh matsala"
"To matsalarmi ke da aka kawo jiya wace irin matsala kenan kodai ya gane ba budurwa ya sameki ba ya maki wulakanci?"
Dariya tayi tace
"Tabbas ya gane ba cikakka nake ba sai dai kinsan baida hurumin ya man maganar ko ya canjaman saboda boka yaman aiki akan haka..."
  Numfasawa tayi tace
"To kodai kin had'u da hatsabibiyar kishiya wadda tafiki MAKIRCI?"
Wata dariya ta saki tace
"Kina tunani akwai wadda zata fini makirci kuwa? Toh in gaya maki ba haka Ramlah take ba in gaya maki kwana d'aya nayi da ita amma nasan wacece ita mace ce mai hak'uri da kawaici."
   Kallo ta bita dashi tace
"Ramlah ki fitoman a mutum ban san inda kika nufa ba..."
    Gyara zama tayi tace
matsalar daga d'iyarshi ne"
"D'iyarshi?"
"Eh"
"Dama yana da d'iya babba ne?"
   Girgiza kai tayi tace
Bazata wuce shekara goma ba"
Dasauri Lash ta mik'e tace
"Shekara 10?"
"Eh"
"Ke ko wace lalacewa tazo maki da yarinyar cikinki zata tada maki hankali?"..

    Zaunar da ita tayi tace
"Kinfi kowa sanin wacece Mufeedah yar ruwan zafi ban da tsoro ko kad'an baka tab'ani ba na k'onaka bare ka tab'ani, kinfi kowa sanin dalilin dayasa na shigo rayuwar Imran na shigone dan na rabashi da farin ciki in tarwatsa gidanshi, da nayi niyar in d'an d'aga masu k'afa amma wannan mara kunyar yarinyar tasa dole zanyi maganinsu da wuri...."
  Ajiyan zuciya tayi tace
"Naji amma mi yarinyar ta maki?"
   Zama ta gyara ta kwashe komai duk abinda ya faru ta gaya mata...
   Dariya Lash tayi tace
"To yanzu miye abinyi?"
     Murmushi tayi tace
"Yauwa yar gari yanzu kikayi magana, wajen boka nake san kije ki gaya mashi komai karki rage komai kice nace so nake ya tarwatsasu ya hana masu farin ciki ya dasa masu bak'in ciki har k'arshen rayuwarsu kingani yanzu babu yanda za'ayi na fita tun da jiya kuka kawoni.."
   (Wa iya zu billahi mi mutane suka d'auki duniya? Shin ko sun manta ana mutuwa ne? Idan ka hana wani farin ciki ribar mi kaci? Kar mu manta akwai ranar sakayya ko Allah bai saka ma wanda ka cuta duniya ba wallahi sai ya saka mashi ranan gobe k'iya, Allah kasa mufi k'arfin zukatanmu..)
   Wata irin dariya Lash tayi tace
"Buk'atarki ta biya, sai dai kinsan saikin kashe kud'i ko?"
Dariya tayi tace
"Kud'i ba matsala ta bace ba ke kin sani"
  Tana gama fad'an haka ta mik'e ta nufi wardrobe d'inta kud'i ta d'auko rapper 1k guda biyu ta wurga matasu tace
"Nasan zasu isheki"
Dariya tayi tace
"Harda canji ma kuwa.. "
     Shewa sukayi suka tab'a...

Don't forget to vote comments share nd follow it really means a lot to me..

MAKIRCI KO ASIRI Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang