BABI NA SHA UKU

1.9K 334 23
                                    

MAKIRCI KO ASIRI

Rubutawa
Yar_ficika

®NWA

Wattpad @yar_ficika
Blog
Phirdauceejeebo.blogspot.com

BABIN NA SHA UKU

K'arasowa wajenshi tayi yana ganinta ya saki murmushi, rungumeta yayi ya saki ajiyar zuciya, janshi tayi ta kaishi d'aki.
"Had'aman ruwan wanka"
Cewar Imran yana kallon Mufeedah
Turo baki tayi tace
"Gaskiya nagaji kawai kaje ka had'a nifa bazan iya yan had'e had'en ruwan wankan nan"
Babu yanda ya iya ya tashi ya nufi toilet...

Fitowa yayi ko inda yake bata kalla ba sai cika take tana batsewa haka ya shirya kanshi yazo ya zauna kusa da ita
"Miyafaru ne?"
Naga kamar kina cikin damuwa, fashewa tayi da kuka tace
"Bayan ka fita Ramlah da Haneefa suka tusani gaba suna zagi kamar ni nace ka tsanesu Ramlah harda marina ita kuma Haneefa tana cewa wai karuwace ni har ciki na zubar kana nazo na aure ka.."
Bata k'arasaba ya tashi yana huci ya nufi d'akin Ramlah

"Ramlah! Ramlah!! Ramlah!!"
Kwalamata kira yakeyi kamar zai tada gidan, k'arasowa tayi dasauri tace
"Lafiya Imran?"
Saukar mari taji a kuncinta kafin ta ankara ya k'ara kwasheta da mari sai da ta saki k'ara d'agowa tayi tace
"Imran mina maka?"
"Aww baki masan mi kikayi ba?"
D'aga kai tayi alamar bata sani ba
"Ubanwa yace ku zagar man mata keda d'iyarki? Har d'iyarki na kiranta karuwa to sai dai idan kece karuwa"
Dasauri ta kalli inda Mufeedah ke tsaye ta hard'e hannuwa tana murmushi, kashe mata ido Mufeedah tayi tana dariyan mugunta. Girgiza kai tayi tace
"Wallahi ba abinda mukayi mata"
"Aww k'arya zata maki lallai Ramlah kin cika annamimiya.."
Hawaye suka kwararo mata tace
"Iya gaskiyata na fad'a maka.."
Cakumota yayi ya d'aga hannu zai k'ara marinta
"Daddy"
jin muryan Haneefa yasa ya kasa k'arasa marin Ramlah wanda takai k'asa sanadiyar hankad'ata da yayi...

K'arasowa tayi inda yake tsaye yana huci, kallonshi tayi tace
"Daddy ka canja ba haka ka saba mana ba baka tab'a yima Ammi fad'a a gabanmu ba, yau gashi kan wata ta nuna Mufeedah tace ka d'auki hannu ka mareta ka jefeta da munanan kalamai akan abinda bata sani ba shin baka gudun Allah ya mata sakayya?" Wallahi Daddy Ammi bata tab'a d'aga ido ta kalli matarka ba da sunan cin fuska amma yau an gaya maka magana ba bincike ka d'aga hannu ka mareta ka aibata ta wanda kafi kowa sanin halin matarka kasan abinda zata iya, ka d'auki hannu ka mareta duk akan wannan munafukar matar taka..."
D'agowa yayi da sauri zai kai ma Haneefa mari sai kuma ya fasa dan duk cikin yaranshi yafisan Haneefa bai san abinda zai tab'ata..
Murmushi tayi tace
"Ni yaka mata ka mara ba Ammi ba saboda Ammi bata da laifi nike gayama matarka magana a yayinda taci fuskar mahaifiyata kuma kasan duk d'an halak bazai bari aci mutuncin mahaifiyarshi ba kuma ban tab'a kiran matarka da karuwa ba kafi kowa sanin irin tarbiyan da kuka bamu..."
Tana fad'an haka ta d'aga Ammi dake ta hawaye suka wuce har sun kai bakin k'ofa ta saki Ammi ta juyo wajen Imran ta duk'a tace
"Daddy idan maganganun dana maka sun b'ata maka rai dan Allah kayafeman, idan wani laifi muka maka muda mahaifiyarmu dan Allah kayi hak'uri kuma da kace baka sanmu ka tsanemu Wallahi mu munasanka muna fatan kadawo Daddynmu nada mai wasa damu mai maida damuwarmu damuwarshi wanda yafi sanmu a kanshi wanda bai iya cin abinci sai muna gabanshi, juyawa tayi wajen Mufeedah tace kinyi nasara amma kijira ranan sakamako Wallahi k'arshenki bazaiyi kyau ba..."
Tana gama fad'an haka ta mik'e takama mahaifiyarta ta kaita d'aki...

Huci Mufeedah keyi tace
"Kanajin yanda d'iyarka ke gayaman magana amma ka kasa d'aukar mataki"
Kallon ta yayi yace
"Bansan miyasa bazan iya bugun Haneefa ba bazan iya aibatata ba Haneefa d'iyatace bazan iya yi mata komai ba kawai dai nasan natsanesu amma bazan iya dukanta ba.."
Harararshi tayi ta buga tsaki ta nufi d'akinta binta yayi yana kira amma bata tanka ba tana shiga ta maida k'ofa ta rufe tanaji yana magiya yana rok'onta amma tak'i kulashi....
K'afafuwanshi yaja ya nufi d'akinshi yana zuwa ya fad'a kan gado yana juyi shi kanshi yasan akwai abinda ke damunshi amma bai sani ba haka ya dinga juyi har bacci ya d'aukeshi..

B'an garen Haneefa kuwa suna shiga d'aki ta fad'a kan Ramlah tana kuka cikin kuka tace
"Ammi kinga abinda nake gaya maki ko? Nace maki matar nan ba matar arziki baceba amma kika kasa yarda da maganata to wallahi idan baki tashi da adua ba nan gaba gidan zata rabaki dashi kamar yanda take ikirari kinaji kina gani zata rabaki da gidanki.."
Jawota Ramlah tayi jikinta suka cigaba da kuka saida sukayi mai isarsu kana sukayi alwalla sukazo suka fara sallah suna kaima Allah kukansu....

Mufeedah na shiga d'aki ta saki uban kuka tace
"Yau ni Mufeedah yar ruwan zafi ake gaya ma magana ban d'auki mataki ba dole in kauda Haneefa daga duniya dan itace babbar matsalata yanzu.."
Haka ta dinga sak'awa da warwarewa daga baya bacci yayi gaba da ita....

BAYAN KWANA UKU
Zaune take gaban boka dumbus tana gaya mashi matsalolinta saida ta gama kaf yayi dariya ya d'ago yace
Mufeedah amarya yanzu mi kikeso ayi masu ne?"
Zama ta gyara tare da jin dad'in yin nasara tace
"Boka so nake ka kauda Haneefa daga duniya ita kuma Ramlah ka saka Imran ya saketa ya koreta ita da yaranta subi duniya daganan gida ya zama nawa nikadai sai yanda nayi..
D'agowa boka dumbus yayi ya kalleta sai kuma ya fashe da wata irin dariya, wadda koni bansan ma'anarta ba...

Wait is like some of my wattpadders basu karanta littafin nan dan basu tab'a wannan yar tauraruwar, while kullum sai na tuna maku kodai labarin baiyin dadi ne na canja wani? Dan abinda kukeso shi nakeso in kuma yana maku dadi pls show me some love, ta danna yar tauraruwar nan thnx y'all

MAKIRCI KO ASIRI Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang