BABI NA ASHIRIN DA UKU

1.8K 174 10
                                    

MAKIRCI KO ASIRI

Rubutawa
Yar_ficika

®️NWA
Wattpad yar_ficika

This page is for you matar Aminina Maryam kwaiseh (Inna Maryama) my personal person, my partner in crime, my annoying babe, my idiot😡 you knw I love you amma kad'an fa🙅🏼‍♀️ nasan zaki tsaneni a wannan page din don't mind me next page zakiji dad'i sai kinyi dariya😇 I love you babe♥️

BABI NA ASHIRIN DA UKU

Haka zaman Imran da Ramlah ya kasance cikin so da k'aunar juna, kullum tattalinta yakeyi, duk abinda Ramlah keso shi Imran keyi baiso ko kad'an ya ganta cikin damuwa. Shekaran Haneefa uku Allah ya k'ara azurta Ramlah da haihuwa inda ta samu namiji, ranan suna yaci suna Alhaji Habeebu amma suna kiranshi da Haneef, haka suka cigaba da kula da yaransu sun basu tarbiya daidai gwargwado, Haneef na da shekara biyu ramlah ta haifi Mukhtar murna waje Imran ba'a magana, yaso ya saka sunan Ahmad sai Ahmad yace mukhtar za'a sa mashi saboda sunan babanshi ne kuma baza'a b'oye mashi ba.
Haka yaran suka taso cikin so da k'aunar iyayensu, duk abinda suke so iyayensu zasuyi masu muddin bai kauce ma fad'ar Allah ba. Kullum cikin yima Ahmad gori Imran yake dan yayi aure, sai dai yayi murmushi yace
"Ina ga matata bata duniya"
Tun rashin auren Ahmad na damun Imran da Ramlah har suka hak'ura suka sa mashi ido, idan Imran ya matsa mashi da cewa ko dan ka haihu ya kamata kayi aure sai yayi dariya yace
"Tunda kai da Ramlah kun haifaman Ai kamar ni na haifesu ne."
Dan dole suka sa mashi ido suka daina mashi maganar aure sai dai kullum suna mashi adu'a Allah ya bashi mata ta gari..

************
Zaune suke parlour suna fira, Mukhtar na saman cinyarta yayi bacci Haneefa da Haneef suna kallon cartoon, kallonshi tayi tace
"Hayatee yau zamu je yawo after isha"
"Ina zamu je?"
Abinda yace mata kenan, murmushi tayi tace
"Wait and see (tsaya ka gani)" girgiza kanshi yayi alamar "to..."
Shirya yaranta tayi cikin shigar k'ananan kaya, Itama shiryawa tayi cikin bak'ar abaya, parlour suka fito inda yake zaune, kallonsu yayi da mamaki
"Wai dagaske kike fita zamuyi?"
Zumb'uro baki tayi tace
"Bana gaya maka ba"
Murmushi yayi ya tashi zuwa yayi daf da ita, ya kama bakin ya murd'e yace
"Sai yaushe zaki san kin girma harda yara uku? Amma kullum k'ara shagwab'a kike"
K'ara ta saki dan bakin har zafi yake mata, sakinta yayi yana dariyan mugunta ya wuce d'aki da gudu ta bishi, suna shiga ya janyo ta da k'arfi ta fad'o jikinshi, marairacewa ta farayi tana ta tuba. Hancinta yaja yace
"Matsoraciyya"
Ita ta taimaka mashi ya shirya shima cikin k'ananan kaya. A jere suka fito kamar sabbin aure, k'arasowa sukayi parlour d'aukar Mukhtar tayi shikuma ya d'aukar mata handbag d'inta ya kama hannun Haneef suka fita.
Suna isa parking space ya bud'e mota Haneef da Haneefa suka shiga mik'a mashi Mukhtar tayi tace
"Bani key"
Ba musu ya karb'i Mukhtar ya mik'a mata key ya shiga mota itama shiga tayi tama motar wuta suka bae haraban gidan....
Basu tsaya ko Ina ba sai wajen salah, suna zuwa tayi parking duk suka fito, sukayi ciki suna isa aka kawo masu menu mik'ama Haneefa tayi ta zab'i abinda zataci, shawarma ta zab'a shima Haneef shi ya zab'a. Kallon Imran tayi tace
"Kai kuma sai abinda na zab'ar maka."
Murmushi yayi yace
"An gama madam"
Dariya tayi ta zab'ar mashi fried rice nd coslow sai ferfesun cow leg, itama shi ta zab'a ta bada order, jim kad'an aka kawo masu suka faraci suna ci suna fira kai da kagansu kasan akwai soyayya mai k'arfi tsakanin wannan familyn. Suna gama ci aka mata bill ta biya tashi sukayi suka fita...
Tunda suka iso hankalinta gaba d'aya ya koma kansu, duk Abinda sukeyi akan idonta gaba d'aya sun gama tafiya da imanin ta ,duniya ji tayi babu wanda ya mata irin Imran lokaci guda kuma taji ta tsani matarshi zata iya komai dan ta rabasu ita kuma ta samu shiga, suna tashi ta tashi ta bisu, daga nesa ta dai dai ta camera d'inta tayi zooming ta d'auki number motar hoto ta koma ciki....
Tana shiga ciki, k'awarta tace
"Mufeedah Ina kikaje?"
Dariya tayi tace
"Sabon kamu nayi"
"Sabon kamu?"
Ta tambayeta dan bata gane maganarta ba. Dariya tayi tace
"Haka nace"
"Ayna kenan? Nidai naga muna nan kuma babu wanda yazo wajenmu."
Murmushi tayi tace
"Baki ga wanda suka zauna nan ba?"
"Nagani"
"To shi naji inaso kuma san da zan iya kauda ko waye ya nemi hanani tarayya dashi.."
Ido ta zaro tace
"Ba gaskia bane ba akwai dai abinda kika hango a wajenshi."
Dariya tayi tace
"Kina da ganewa gaskia ne daga ganinshi yana da abun hannunshi ni kuma kinsan duk hannu mai maik'o shi nake bi.."
"Amma Mufeedah kina ganin zaki samu shiga wajen shi? Jifa yanda yake tarairayan matarshi da d'iyanta."
Dariya tayi tace
"Lash kin manta wacece Mufeedah kenan kin manta Ban tab'a neman abu na rasa ba, Bari in gaya maki tunda na kalli matarshi naji na tsaneta dan haka ko ta halin k'ak'a Sai na shiga gidan mutumin nan sai na tarwatsa gidanshi na dasa masu bak'in ciki daga nan nikuma in kwashe kud'inshi in k'ara gaba, shiyasa na bisu na d'auki number motarshi hoto dan gobe asuba gurin boka na kan dumbus zataman.."
Dariya Lash tayi tace
"Nasan zakiyi fiye da haka akan abinda kikeso to banda shakku akanki."
Tab'awa sukayi suna dariya....

MAKIRCI KO ASIRI Donde viven las historias. Descúbrelo ahora