16

863 89 1
                                    

DABAIBAYI👄

©Khadija Ahmad (Kdeey😊)
WATTPAD @Deejaht ahmad

®Haske writers association 💡
(Home of expert and perfect writers)

                          (16)

*NOT EDITED *

Da ya dawo daga masallaci be zarce ko ina ba se bakin shagon dake daura da gidan su, hira wasu Samaria biyu keyi da wasu daga ma’aikatan shagon hirar dai ta ball ce shi dai daga ya murmusa se ya d’aga musu kai idan an tambayesa abu dan Sam shi ba ma’abocin kallon kwallon qafa bane, wayar sa dake aljihu ya zaro ya shiga yanar gizo ba komai yana duba nasarorin da kamfanin sa ke samu a can qasar ta UK.

Kewar kimberly ta tsargo masa, tsam ya miqe tare da zagawa bayan shagon dan kiranta sosai yake son jin muryar ta,
Ilai kuwa tana d’agawa ta fashe masa da kuka, se dai tun kan ya samu damar rarrashin ta wata mota ta d’au hankalinsa wacce tayi parking daidai qofar gidan su, duk da irin kalar hello da take sirfa mishi be samu damar kulata ba, ya kashe wayar tare da seta wayar shi ya d’auki hoton plate number d’in,

Tsayuwar shi ya gyara , ya shiga dialling number bello ringing d’aya tayi ya d’aga “kana ina”

“‘Daki doing what suits me best”

“Ok duba cikin wayar na turo maka saqo ka turawa dss bashari ya duba min”

“Yes broseee”

Kashe wayar yayi, ya cigaba da karantar motar zuwa can yaga anja an tafi, numfasawa yayi a hankali kan ya ja qafa ya koma cikin gida dan ji yayi komai ya sare mishi, me ke shirin faruwa kuma? Tambayar datayi crossing mind d’insa kenan.

*
Misalin 7:45 am zaune suke bisa dining table suna breakfast shiru ya ratsa, gyaran muryar uncle ce taja hankulan su duka, inaso wani cikin ku yaje gidan su Sam ya shaidawa gwaggo Ina willing kai yaranta boarding school saboda wasu dalilai nawa and bana so taqi aminta so kuyi duk abinda kuka san zaku iya saboda ta aminta” ya miqe dai dai lokacin shima anwar ya miqe

“Uncle ni zanje na qarasa processing visa d’inka”

Kallonshi yayi “Luke gidan tare idan ka dawo kayi wannan d’in daga baya” ya wuce ya barsu dariyar data kamo bello ya guntse ta dan yasan hanya hanya Anwar keyi dan kar su had’u da gwaggo domino uncle ya fad’a masa cewa ya shaida wa gwaggo abinda yayi wa ‘yar ta.

***
Tafe suke a hanyar su ta dawo wa daga aiken da gwaggo tayi musu , munu ta dage se bawa Sam labarin da wani littafin hausa da wata ‘yar ajinsu ta basu take daf zasu tsallaka kwaltar titin gidan kawu kabiru ta hango wani mutumi ya shiga gidan, nuna wa munu tayi, “zo muje mu ga wane munu, kar ayi wa su umma sata”

Bin ta munu tayi suka tafi a hankali suka karkata suka shige gidan sad’af sad’af yacce baza a ji takunsu ba falon farko suka shiga ba kowa nan suka lelleqa ko ina ba alamun mutum d’akin amir suka fad’a jin kamar takun mutum, can suka jiyo wata murya na waya
  “It’s cleared ma!”
Daga cikin wayar suka jiyo ance “I am very sure zasu dawo ko ba dad’e ko ba jima just don’t forget to keep an eye”

“Yes ma! Amma ya batun samira fa?”

Dariya aka kyakyace da ita “wannan ka barta har zuwa lokacin da zata mallaki hankalinta shine take me amfani, yanzu ita da hoto basu da maraba”

Firgici me sunan firgici ya kama Sam da munu suka ruqunqume juna har basu sani ba suka bigi wani flower vase ya fad’i qasa ai a guje suka maqale jikin bango se dai jinginar su ke da wuya bango ya juya dasu se gasu cikin wani tamfatsetsen closet wanda yasa lokaci d’aya Sam ta kurma wani uban ihu me tada hankali

Munu dake a firgice tayi saurin d’ora hannunta a bakin Sam “shii shii...k...iy..I shi..ru kar ..a ji mu Sam”
Ta fashe da kuka qasa qasa, hannun da Sam ke pointing tabi da ido bata san lokacin da ta  fad’a baya ba har ta bige da bango,

“Shish..shine...”

Yawu munu ta had’iye da qyar idanunta kafe kan fuskar zakin dake kallo su, numfashi ta shiga saukewa a hankali ta taka a hankula zuwa wurin fuskar ta yaye saurin ja baya tayi ganin hoton ya habiibii,

Saurin kallon juna sukayi cike da mamaki Sam cikin raunanniyar murya tace “dama shi..ne “ munu ta matsa kusa da ita tare da jan hannunta suka nufi wata qofa a hankali suka murd’a key d’in jiki se gasu a waje,wajen ma dai dai layin gidan gwaggo fita sukayi da sauri ba kowa se tsirarun mutane juyawa sukayi suna kallon qofar data rufe bazaka ta’ba cewa akwai wata qofa a wurin ba a kid’ime suka shiga zabga sauri zasu shiga gida kenan su mu’allim bello suka iso.

A tsakar gida suka tarar da gwaggo suka fad’a mata suna kuka, duk suka rikita ta, menene? Me ya faru? Me ya same ku? Amma shiru ba wanda ya kulata, sallamar su Anwar ce ta sa su sassautawa

“Yawwa ai gara da kuka zo, kun gansu sun tisa ni gaba se tambayar su nake ba wanda ya kulani, dan Allah kuntayani tambayar su, oh ni haulatu”

Mu’allim bello yace “Sam, munu what’s wrong? Meke damunku?” Nan ma shiru ba amsa carpet d’in dake ajiye a gefe ya shimfid’a yana me kallon Anwar.

Anwar da duk suka qular dashi jin yanda ake faman tambayar su basu amsa ba ya ce “Idan baku had’iye kukan nan ba, ni da ku ne” cikin kakausar murya,

‘Dif kake ji wai malam yaci shirwa, ashe wargi ma wuri ya samo “ku samu wuri” sum sum sum suka zauna kusa da gwaggo yaci gaba before the count of 3 ku fad’i abinda ke damun ku.

Tar tar tar suka zayyano abinda ya faru hawaye na biyo baya tun bare Sam, hankali tashe gwaggo ta rinqa salati tana sallallami fad’i take “shikenan zaman mu a garin nan ya qare oh ni Allah ka bani ikon cin jarabawar nan taka, yanzu ace habibii ne dama ke qoqarin lalata miki rayuwa, kai duniya ina zaki damu” ta fashe da wani marayan kuka ta rungumo su jikinta

“Ba kuka zaki yi ba gwaggo”

“Me kake so nayi, bani da kowa bani da komai d’an uwana ya gujeni wannan yaran kawai nake gani naji dad’i to suma ana neman fara farautar su ina zanso kaina ni haulatu”

Qwallar data ciko idanunsa ya share “gwaggo ku tashi mu tafi”

Bello yayi saurin kallonsa, “ina?”

Gidan mu “zaman su a nan ya qare”

Ta girgiza kai “um um d’an nan wahalar  se tayi yawa, ka bari zuwa gobe se mu koma can garin mu, inda muka fi wayo”

“Gwaggo dan darajar Allah ki tashi mu tafi in yaso Mayi deciding step to take next”

Kallonshi tayi ido a kod’e “kuj’e d’aki ku d’auko mana hijabai”

Qulle gidan su kayi, suka d’unguma zuwa kwairanga road.

©Kdeey😊

DABAIBAYI (COMPLETED)✅Where stories live. Discover now