No 22

854 33 1
                                    

💦💦💦💦💦💦💦
           💦💦💦💦
                      💦💦







*ƘAWAR ƳATA CE*
    *1441H/2019M.*


®☄
*GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍🏻*
_{Gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata burin mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da lahira}_

     '''🎐G•W•A🎐'''
_*GASKIYA DOKIN ƘARFE•*_



Story & Written
         By
*SUMMY M NA'IGE*✍🏻


*Didicated to..*
*All Gaskiya writers*😘


~VOTE & FOLLOW 4 Wattpad@GaskiyaWritersAsso.~

*A RAYUWA ILIMI NA DA DAƊI IDAN KASAMU ƘARAN CIN  ƊAYA DAGA CIKIN BIYU NAN RAYUWA BAZATAYI DAƊI BA, AllAH KABAMU IKON NEMAN ILIMIN DUNIYA DA LAFIRA*
*AMEEN YA AllAH.🙏*


*Page 49*


*_________*📖 Kanta ta ɗago ta kalleshi shiko inba huci ba ba'abunda ya keyi.

Nunin ta ya keyi da ɗan yatsa kana yace "kigaya min me kika ba yarana wanda ke neman ya ka shesu".

Komai bata ce masa ba dan irin yadda taga yana magana ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba.

Tashi tayi taje nesa kaɗan dashi ta kira Hajiya Sa'a ta faɗa mata abunda ke faru.

Bata jima da kiran taba sai gata tazo .

Yadda taga Daddy ko ita hankalin ta ya tashi amma ta dake ta fara bashi haƙuri da nuna masa cewa yaran zasu ta shi.


Cikin ikon Allah yaran na cika awa uku suka fara mutsawa.

Doctor suka kira ya ƙara duba yaran ya tabbatar musu da lafiyar su sannan Daddy ya samu natsowa.


Daddy ko ya nace sai Fatima ta gaya masa me taba yaran shi.

Badan taso ba tayi masa bayani tace bata basu komai ba inba Kulsum da tace Mumy ta basu madara ba.
.


Ai tun bata ƙarasa faɗa ba ya kama hanyar fita Hajiya Sa'a na kiran sa amma  bai san tanayi ba.


Sosai yasa direba gudu basu ɗau wani lokaci ba suka ƙarasu gidan.

Kafin driver yayi packing Daddy ya buɗe murfin mota yafito.

Ba kowa a parlour dan haka da sauri ya ƙarasa part ɗin Mumy .

Koda yaje har zai ƙwalamata kira sai yaji tana waya haɗe da wata irin dariya .

Bai ce komai ba dan abun mamaki ya bashi na wannan dariyar da takeyi.


Wayar ta taci gaba da yi ita da Hajiya Shafa tana bata labarin yadda akayi taba yaran poisen suka sha har yadda taje wajan wani Malami wanda yace a cikin satin nan Daddy sai ya sake Fatima kome suke ta ƙama da shi .

Firar su suka cigaba dayi sai da suka gama kana suka aje wayar Mumy tayi haka ta ɗago kanta suka haɗa ido da Daddy aikuwa ba shiri ta tashi zaune tana burin kunya.


Shiko Daddy gaba ki ɗaya yarasa me zai ce mata abun duniya ya taru yayi masa tsaye azuciya .


Mumy ko gaba ki ɗaya jikin ta yafara karkarwa harda kukan munafurci ta farayi.

Har ta buɗe baki dumin tayi masa magana amma ya daka mata tsawa yace "duk abunda zaki faɗa bana son ji,dan haka kitashi kibarmin gidana na sakeki saki biyu, kuma kisani  komai kikayi min na barki da Allah kuma kanki kika cuta bani ba".


ƘAWAR ƳATA CE                              {COMPLETED 01/2020.}   Where stories live. Discover now