33

489 30 0
                                    

*NAYI DACE*

Maryam💕
Wattpad@ mamsuhaimerh

*33*
          *comments naku su ke motivating dinai naci gaba, Ina Jin dad'in comments naku ko da ban samu nayi reply duka ba, love you toos😍😍*

Sai bayan la'asar Sultana ta tafi ta barmin Huda, bayan tafiyarta na zauna na fara tunani, idan har na ri'ke Huda to kenan inada hope na komawa ga Saleh? Gashi har na kwana a gida bai nemeni ba, idan har inaso na cire Saleh a rayuwata sai na rabu da duk wani abu da ya danganceshi.

Huda na bacci mama ta dawo ta sanarmin Ru'kayya ta haifi mace, d'aukan Huda nayi na fice na nufi babban gida, babu kowa a gidan daga ita sai adda da Yaya dake had'a ruwan zafi ita Kuma tana d'aki tana zaune tana waya sai wani lullumshe Ido takeyi, d'aukan babyn nayi ta ajiye wayar tareda kallona tace "Bilki yaushe kika zo babu labari?"

"Jiya" na fad'a ina gyara Safar babyn, zubamin ido tayi tace "bakida lafiya ne? Naga kin canza". Murmushi nayi mata na girgiza kai alamar a'a, wasa ta fara da Huda ganin banida niyyar magana, ganin shirun yayi yawa nace mata "mun rabu da Saleh jiya na dawo gida".

Kallona tayi cike da tausayawa abinda banaso kenan, banaso ana tausayamin hakan ke sakawa Ina tausayawa kaina, dafa kafad'ata tayi tace "Ayya Bilki kiyi ha'kuri Allah yasa hakan ne mafi alkhairi"

"Ameen nagode" na fad'a tareda 'ka'kalo murmushi, Ru'kayya ta san irin zaman da nakeyi dukda ba komai ta sani ba, ta san dai matsalar rashin haihuwa da kuma 'kiyayyar dangi, da ace ina haihuwa wani wula'kancin ba'a isa a yimin shi ba.

Bansan cewa da 'karfi na furta maganar ba saida naji Ru'kayya tace "a'a ki ma dena wannan tunanin bilki, idan ba'a sonka hausawa suka ce sai ka shiga ruwa ace ka tada 'kura, ko kina haihuwar abinda Allah ya tsara sai ya faru sai ya faru, sai ace kin fiye haihuwa ko ace kin fiye haifar maza ko Mata, ko ace 'ya'yanki basuda tarbiyya ko Basu da kyau ko 'kazamai ne, d'an adam ba'a iya masa ke dai kuyita addu'a Allah yayi miki za'bin alkhairi ya kuma saka miki, amma kuma kun rabu kika taho musu da yarinya?"

Kallon Huda nayi nace "gani nayi kamar idan na taho da ita zata ragemin kewa kuma..."

Shiru nayi Ru'kayya tace "a'a indai gaskiya zan fad'a miki babu fa'idar tahowa da yarinyarnan, kina tunanin watarana zaki koma kenan ko? Kinada hope kwanannan zai maidake ko? Bilkisu na rasa wace irin zuciya ke gareki, ko da tilastashi akayi ya sakeki karki sakawa ranki cewar zaki koma domin mazan yanzu wallahi sun 'baci, duk son da namiji ke miki wuyarta ya furta sakinnan sai Kinga banbanci, idan kika ri'ke yarinyarnan kamar bakyaso kin ri'ke wani sashi ne na 'kaddararki mara kyau, babu ke babu kwanciyar hankali indai Zaki kalleta to zaki tuna iyayenta, ki tuna tsohon mijinki sannan ki tuna irin 'kuncin da kika shiga ta dalilin jininta, indai kece bilkisun da na sani kina dab da fara Jin haushin yarinyarnan, shawarata idan kinaso ki manta da baya to ki maidata wajen iyayenta, bakya ganin wasu idan an sakesu 'ya'yan cikinsu ma barinsu suke saboda basa son abinda zai tuna musu da rayuwar aurensu, ki maidata kya dinga ganinta a hoto zaifi miki gaskiya a ganina, amma kiyi tunani".

Ko da na kwanta bacci tunanin maganar Sultana da Ru'kayya nayi, tabbas inada son kaina a wannan lamari bana hangen kowa sai kaina, ta yaya zan cirewa kaina wannan damuwar domin banaso ta shafi kowa nawa, hawaye ne ya gangaromin na goge, sallamar mama naji da sauri na rufe idona kamar bacci nakeyi, sunana ta kira nayi shiru ina jin takunta tana matsowa dab dani ta d'aura hannunta a kaina, numfashi ta sauke tace "Allah ya kyauta" sannan ta ajiyemin abu a gefen gadona ta fita, juyawa nayi naga pcm na d'auka nasha domin kaina na ciwo na koma na kwanta na rufe ido ina jiran zuwan bacci saidai kamar nasha maganin hana bacci, na san cewa ina gab da bawa kaina matsala idan har bana cikakken bacci da cin abinci, a cikin jikina ma na fara Jin na canza.

Wasa-wasa har nayi kwana biyar a gida Saleh bai le'ko ba balle waya, Ina zaune a Palo na zubawa tv ido naji sallamar aunty, amsawa nayi na gyara zamana, tana shigowa ta ri'ke 'kugu ta zubamin ido take tsoro ya kamani nasan yau zuwan nawa ne na musamman, " 'kaniyarki" ta fad'a tareda yimin da'kuwa, turo baki nayi nace "ni kuma anty me nayi?"

NAYI DACE.Where stories live. Discover now