39

540 31 1
                                    

*NAYI DACE*

Maryam💕
Wattpad@ mamsuhaimerh

*39*
             Matsowa ya fara yi dai-dai lokacin da Aalee ya fito, dafa kafad'ata Aalee yayi yace "haba sweet B yanzu fushi kikayi sosai? Am sorry kema kinsan da wasa nakeyi bansan cewa har yanzu wannan is a sensitive topic to you ba".

Gaba d'aya hankalina na kan Saleh, Aalee ganin ban kalleshi ya sanya ya saka hannunsa biyu ya tallafo fuskata tareda juyota gareshi, murmushi yayimin wanda ya bayyanar da kyawawan dimples d'insa yace "look into my eyes and say you forgive me baby, bazan kuma ba kinji?" Ya Kare maganar yana turo baki, kallon Saleh na sakeyi da idanunsa a take suka sauya da alamin kishi, wani irin kallo yake ma Aalee wanda baisan ma yanayi ba hakanan naji wannan lokaci yayimin dai-dai.

Cire hannun Aalee nayi daga fuskata nace "na yafe maka, idan kuma ka kuma...." Jan kunnensa nayi ya saki wani 'kara had'e da murmushi, kama hannunsa nayi na nufi 'kofa cikin sauri Saleh ya matso tareda kama 'kofar, a fusace ya kalli hannuna dake ri'ke da na Aalee sannan yace "me kikeyi haka Bilkisu?"

Shigewa gabana Aalee yayi yace "easy man, no one talks to my girl without my permission".

Tamkar Saleh zai daki Aalee yace "malam matsa da matata nake magana".

Bansan lokacin da dariya ta 'kwacemin ba na girgiza kai tareda jan Aalee nace "mu tafi kar mu makara". Shigewa gida nayi na doka 'kofar saida Aliyu ha d'an tsorata, knocking Saleh keyi yayin da nake jingine jikin 'kofar yanda zuciyata ke bugawa abun har tsoro ya bani, ban ta'ba tunanin ganin Saleh a wannan lokacin ba kuma banda Allah ya kawo Aalee bansan ta yaya zan fuskanci sale ba, hannuna na Sanya a 'kirjina tareda sauke numfashi ina jin bugun Saleh har cikin kaina.

Fitowa su Raudah sukayi tareda Aunty tace "waye yake mana bugu a gida?"

"Ba kowa"

"Tsohon mijin Aunty B ne" mukayi maganar a lokaci d'aya, cikin sauri aunty ta nufo 'kofar take yanayinta ya canza, bansan lokacin da na ri'ke hannunta ba.

Girgiza mata kai nayi a hankali nace "dan Allah Aunty a'a". Hard'e hannunta tayi a 'kirji tace "a yanzun ma kareshi kikeyi?"

Muryata tana rawa amma a haka na dake nace "a'a Aunty ba kareshi nake ba, amma bashida matsayin da zaki saurareshi a wurinnan jannat ce kawai dai-dai dashi, ki kyaleshi dan Allah bansan ma da rayuwarsa a wurin ba".

Dafa kafad'ata tayi tareda murmushi sannan ta juya ta koma gida, runtse ido nayi tareda maida numfashina na bar 'kofar gate d'in da murmushi a fuskata, bud'e gate d'in mai gadi yayi duk muka shiga mota bansan yanda na 'kare a passenger seat ba au Raudah kuma suna baya dukkansu, a tsaye naga Saleh ko kallo bai isheni ba muka wuce.

Mun kusa 10mins babu wanda yayi magana, jannat ce tayi breaking silence d'in tace "ya Aalee Ina zamuje wai".

Kallona yayi yace "Aunty B zaki tambaya".

Kaina na window nace "inaso na sayi kayan makeup, takalma da jakunkuna". Bansan inda zan samu abubuwan da nake bu'kata ba saboda haka muka yita yawo a gari har na samu wurin jakunkuna masu matu'kar kyau, guda biyar na siya su Raudah suka sayi d'ai-d'ai, muna zuwa wajen biya Aalee ya mi'ka katinsa, wurga masa harara nayi na kar'bi katin na mi'ka nawa.

Raudah dake bayana ce ta kar'bi katin ta mi'ka tace "kin ta'ba ganin inda aka fita da namiji mace tayi siyayya?"

Cashier d'in har mun fara b'ata rai, kallon Raudah nayi nace "tunda nace zan biya ki barni kawai dan Allah, na dad'e da kud'innan bansan me zanyi dasu ba kuma abin kashewa yazo sai ace bazan kashe ba?"

Ja tayi da baya ta barni na biya, a kusa da shagon na sayi takalma su Raudah suka 'ki saya saboda basaso na biya, da kyar suka amince suka d'auki d'ai-d'ai shima saida nace zamuyi splitting kud'in da Aalee.

NAYI DACE.Where stories live. Discover now