38

501 29 1
                                    

*NAYI DACE*

Maryam💕
Wattpad@ mamsuhaimerh

*38*
            "oh" ta fad'a tareda maida hankalinta kan waya, bayan ta gama dannawa ta ajiye ta kalleni tace "ya kikaji?"

"A me fa?" Na tambaya tareda tashi na zauna, "mutuwar aure, how does it feel?"

Shiru nayi ina tunanin yanda zan bata amsa, tunda aurena ya mutu babu wanda ya ta'ba min wannan tambayar dukda mama da aunty sun kula dani sosai, amma ba sa'annina bane da zasu tambayeni yanda mutuwar aure take, abinda suke tambayata shine kina lafiya? Saboda kar damuwa tayimin yawa.

Zama nayi na had'e hannayena a gwiwata nace "umm to naji abubuwa da yawa ban ma san yanda zan fasalta su ba".

Idanunta na kaina tace "baki ta'ba fad'awa kowa ba kenan". Gyad'a kai nayi alamun eh ta juyo gaba d'aya ta maido hankalinta kaina tace "nima nan da kike ganina bazawara ce na miki ta hausawa, amma bansan zafin mutuwar aure ba saboda ni da aurena ma ya mutu bansan ya mutu ba sai bayan almost 6months, shiyasa nake tambayarki i can see how hurt you are Bilkisu".

Numfashi naja na sauke sannan nace "a wajena it was the worst feeling ever, I feel sad, hurt, rejected, guilty,...I feel so many things at the same time gaba d'aya 'kwa'kwalwata kamar an dakatar da ita daga aiki, ko processing abinda ya faru na kasa yi a kaina kalmar ce kawai ke min yawo, sai bayan na koma gida Mama ta tasomin da maganar sannan na fara jin zafin abinda ya faru, Raudah muna matu'kar son junanmu, mun yarda da juna,idan muna tare gaba d'aya mantawa muke da kowa da komai, abinda ya girgiza ni shine yanda a cikin mintina kad'an shekarun da mukayi suka tashi a banza".

Saurarona takeyi yayin da na bata labarin abinda ya faru itama take sanarmin dalilin nata mutuwar auren, rayuwarta abin tausayi dukda ta tsayawa kanta ta kuma kare , tayi fighting ma right d'inta har 'karshe, kuma ita dangin mijinta na sonta sosai unlike me.

Har 12 muna hira kuma naji dad'i sosai, domin da iddata ta matso 'karewa kullum tunanin Saleh nakeyi, a cikin fargaba nake idan na gama idda wacce irin rayuwa zan fara, ya zanji idan Saleh ya dawo rayuwata bayan na gama tsarata na cireshi daga lissafi na?

Hannun Raudah naji a kafad'ata tacemin "Bilkisu ba laifi bane ka so mutumin da ya cutar da kai, kuma yanda kika bani labarin zamanku zaiyi wuya ace baya missing d'inki fiye ma da yanda kike missing d'insa tunda ke mace ce shi Namiji ne, na sani zai nemeki ko kusa ko nesa, kawai kiyi preparing kanki yanda Zaki kar'beshi, kina son ya koma rayuwarki ko kinaso ki canza rayuwa it's up to you, balle ma kwanaki kad'an suka rage da zarar igiyar aurensa ta sauka daga kanki ke a jikinki sai kinji sauyi, yanzu ragowar hormones d'insa da ke jikinki su ke sanyaki wannan damuwar amma trust me da kin gama idda zaki samu sau'ki insha Allah".

"Thank you" na fad'a tareda share 'kwallar da ta zubomin, banason tunanin rabuwa da Saleh amma abinda Allah yayi baka da ikon canzawa.

Washegari babu wani abu da muka yi, a kwance na wuni saidai nayi bacci na farka na gyara kwanciyata na sake komawa bacci, breakfast ma a d'aki nayi zazza'bi ne sosai a jikina.

Muna parlour muna hira Aunty ta le'ko tace min "ya kamata yau muyi celebration fa".

Juyawa mukayi duk muna kallonta Raudah tace "au Aunty sai yau zakiyi celebrating zuwanmu? Har munyi kwana biyar?"

Zama Aunty tayi a gefena tace "celebrating 'yata ta zama sakakkiyar tsuntsuwa mana ni ina ruwana da ku, celebration zamuyi na fitar Bilkisu daga idda". Hannu biyu na saka na rufe fuskata nace "Aunty dan Allah ki bari mana".

"Da gaskiyar aunty, yau ranar taki ce dan haka ki fad'a mana abinda kikeso". Raudah ta fad'a tareda zama a kusa dani, twins kuwa har sun fara rige-rigen shiga wanka Aalee kuma idonsa na kaina duk jira suke suji me zance, nasan basa son zaman gida sannan nima akwai abinda nakeso na siya, jingina nayi a bango nace "shikenan ku shirya mu fita".

NAYI DACE.Where stories live. Discover now