town

34 3 0
                                    

JINAH MATAR ALJAN BOOK2 EP11 DAN KARIN BAYANI KUNE MEMU TA SHAFIKAN MU KO NUMBER(09037786636) EP11( N AND N)Idan muka koma bangaransu aya kuwa lokacin da noor najib sawiris tace dasu sun karaso cikin (mysterious) city dukkansu lekawa kasa sukai suna kallon yanayin garin ayace ta dago da kanta ta kalli ayu tana me cewa kalli yadda aka tsara ginin birnin,nan daga gani kasan cewa asalin maginan sunfuto ne daga birnin misira yananyin ginin da salon duk irin na canne sai dai ban bance 2 da yawa dake cikin mysterious city din kalli can tana me nunawa da hannunta tana mai cewa can wata katuwar pyramid CE a tsakiyar garin wacce zata iya fin ta Giza pyramid girma sau kamar goma itace kamar a tsakiyar mysterious city din kuma duk girmanta an mata fenti da zallan ruwan gold tun daga nesa idan hasken rana ya daki jiki sai kaga tana wani irin kyalli mai ban sha"awa Wani abun mamaki kuma tsakiyar garin ba bishiya ko daya wani irin salo sukaiwa hanyar ta Inda aka baza wani dabe Wanda akayishi da ruwan zinare duk inda ka taka kana dauke kafarka zakaga wajen yana kara kyau da sheki gefe da gefen garin kuma nan ne suke da wayansu irin lambuna ga wata ciyawa da ta zagaye ko ina kore shar 2 acikin ko wane lambu zaka sami wata katuwar bishiya kamar guda biyar wacce tsakiyar bishiyar daga gan gar jikinta anan akai wata kofa saman bishiyar kuma gidane guda wanda akai masa wani salo a mul mule yake gidan kamar football ko ina ganyan bishiya ya rufe shi ga wasu futulu masu haske inda zaka shiga shashin nan da kaida bakin cikin har abada. Lokacin da su malam najib sawiris suka sauka kan Dan daryar wannan daben zinaren sai suka futo daga cikin keken, suka nausa cikin wannan golden pyramid din suna masu kalle 2 kamar wasu yan kauye koda suka shiga cikin garin saiga wata na,ura mai kira kamar faranti ta tawo wajen mu nan aljani akeem ya hau kai tare da nu na mana muma muhau nan kwa batare da bata lokaci ba muma muka haye da ga nan sai ta fara ta fiya a nutse daga kasan wannan farantin na urar wani irin ta kalmine na karfe ya futo ya zagaye kafar mu sannan abun ya kara gudu zuwa cikin golden pyramid sai da muka dau lokaci mai tsawo kafin mu karaso wajen wayansu dakuna  guda uku masu kofa iri daya sannan abun ya tsaya mu kuma muka sauka daga kai alokacinne aljani akeem yace wayannan dakunan anan ake tsaron ruhin sarki Khufu da kuma jar hukar sihiri sannan a wannan dakin na tsakiya anan ne gawar sarki Khufu take ajiye Ku biyoni zuwa cikin dakin da kwalbar ruhin sarkin Khufu take don mu tattauna game da yadda zamu tsira daga sharrin uwar bokayan duniya bokanya zarishat. OK muje don ni nama Dade da gajiya yau kusan kwana 5 bamu hutaba abunda mayah tace kenan lokacinda suke gabda shiga cikin daki nafisa ce tace au har mun kai kwana kusan 5 ahanya kenan eh ki duba wayarki ki gani yau kwananmu hudu da kusan awa 14 tam gaskiya kuwa wannan garin na daban ne inji malik Muhammad sawiris eh daman kusan yanayin duniyar mu ta aljanu da taku da ban banci haka sarkin aljanu malik ya fada adai2 lokacin da suka karaso dai 2 wajen wani katon table Wanda aka zaga yeshi da kujeru na alfarma wa yanda suka sha kwaliya da zinare kan kujerun wasu mayaka ne su kimanin su Dari daga karshan table din kuwa wasu teburane guda uku amma ta tsakiyar tafi ko wacce girma da ado sukwa biyun da suke gefen dama da hagu wani jarimine Wanda ya kasance shine sarkin yakin birnin Khufu a kujera ta hagu ta dama kuma wani Maya kine Wanda kana kallonsa kasan cewa lallai ya futone daga nayiyar birnin sin wannan kujerar kuwa ta tsakiya itace ta sarkin aljanu akeem a karshen daya bangaren table din kuma anan aka saka  Kujeru guda takwas sune wajen zaman su najib sawiris tare da tawagar su. sarkin aljanu akeem ne ya yi musu iso akan su zauna akan wayannan kujerun nan  suka zazzauna har a wannan lokacin wayannan zakwakure dakarun yakin na birnin Khufu kowanne yana tsaye akusa da kujerar sa sai da su najib sawiris suka zazzauna sannan sarkin aljanu akeem ya je wa kujerarsa ya zauna koda ya zauna sai suma ragowar dakarun suka zauna sannan wani daga cikin su ya tashi yana me cewa jin jina wa sarki akeem sannan yace barka da zuwa ya Ku zuriar sarki Khufu koda yazo nan a maganarsa sai ya dauko wata takarda ya war wareta ya fara karantawa kamar haka.Daga masana da masu tsaron yankin kasar mu ta birnin Khufu sunce asanar da kai cewa ayau dinnan bokanya zarishat tabar tsuburin aljani ra,asu tare da jama,arta takuma sami hadin kan aljani ra,asu karkashin jagorancin bokanya Hindu wacce ta kasance yayar ka. masanan sun bada lokaci sunce indai ba a dau mata kiba to komai na iya faruwa, sunce nan da kwana uku dolene a tari su bokanya zarishat a hanya kafin su karaso cikin garin nan namu sannan kuma dole a yi kyakkyawan shiri don duk yadda muke zaton girman abunda zamu fuskanta yafi haka daga karshe wasikar tana kara cewa kwana ukune a gaban mu Daga haka sai ya kara risinawa sannan ya nemi waje ya zauna A wannan lokacin ne sarkin aljani akeem ya yi garen murya yana me cewa ina sarkin yaki nan take sarkin yaki yatashi yana mai risinawa agaban sarki yana cewa gani ran sarki ya Dade aljani akeem yace menene shirinka game da tunkarar abokan gaba Allah ya taimaki sarki mun Riga mun gama shirin mu kawai jiran taba kinka muke muna da zakwakuran mayaka dubu dari tare da kayan yaki da makamai kala kala kawai abunda ya rage mana muji ta bakinka nan sarki akeem ya kara cewa ina sarkin malamai nan sarkin malamai ya tashi yana mai risinawa sannan yace ran sarki ya Dade game da ban garena yau kimanin wata daya kenan muka fara saukar alkur,ani mai sarki don neman tsira daga mugaye sannan. Sarkin makera ya kawo mana duk ilahirin kayan da suka kera mu kuma muka tufe su da addu,o e don tsari daga dukkan muya gun abokan gaba daga karshe dai ya mai girma sarki kawai umar ninka muke jira don tuni duk mun gama shirin komai nan ya kara risinawa sannan ya zauna koda ya zauna sai sarki akeem yay garen murya sannan yace ya manyan bakin mu ababan girmamawa barka da zuwa birnin Khufu (mysterious city) kuma nasan yanzu HK kunji duk yadda muka tattauna game da wannan babban jihadi da zamuyi na hana masu so suyi zalunci adoran kasa yin zalinci kamar yadda kukaji saura kwana uku ya rage mana to gobe duk za,a kammala hada kayan yaki bisa ababan hawan mu da daddaren gobe zamu tafi zuwa bakin kofar birnin nan mu kafa tarkuna da sauran dabarun cin yaki kafin su karaso mu mujirasu na sani cewa mutane ukune a cikin Ku suka iya yaki daga aya sai ayu sai malam najib sawiris to mun tanadi wata na ura wacce zata tai maka muku wajen kariya daga abokan gaba kasancewar yanzu lokaci ya kure ga shi kuma kuna bukatar Hutu sabo da haka anan zamu rabu daku zan hada Ku da jarimi halanchal nan wannan na gefen daman sarkin aljanu akeem ya tashi yana rusinawa sannan ya fara magana cikin salon da kanaji kasan ya futone daga yankin birnin sin cewa yayi cikin muryar girmamawa kamar yadda kukaji sunana halanchal na futone daga kasar sin wato China baba na ne sarkin gargajiyar,kasar ,kuma,uwata takasance Aljana atakaice dai ni ruwa 2 ne rabi mutum rabi aljan kamar su aya da ayu to amma kasancewar babana ne mutum ba uwata ba ban sami irin karfin da kuke dashiba Abu daya nasan na kware dashi sosai shine iya yaki acikin duniyar aljanu tun banfi shekar 7 ba uwata ta kaini wajen sarki aljanun birnin sin ban dawo gida ba saida na kai shekara 20 wannan shine Dan ta kaitaccen lbr na tunda nafisa taga wannan mutumin taji duk duniya babu Wanda taji ya kwanta mata irinsa haka kawai takeji wani bugawar zuciya in suka hada ido a bangaren jarimi halanchal ma kusan hakan ne shiyasa ya saukar da Kansa kasa yayin da yake musu bayanin shi waye. sarkin aljanu akeem ne yace yakai jarimi halanchal ina mai umartar ka da ka kasance da su malam najib sawiris ka za ma mai kare lafiyar su kafin jibi na baka amanar su akanka ka kula dasu duk da nasan ba abunda zai samesu amma dai duk acikin Karin tsarone nasani koba aya da ayu malam najib sawiris zai kula dasu nan take sarkin aljanu akeem ya tashi tsaye yayinda dakarun nan dasuke cikin dakin suka Riga shi tashi suna masu nuna biyayya agareshi zaga yowa yayi wajen su malam najib sawiris yai musu sallama sannan shida sarkin yakin sa suka futa daga cikin dakin a dai dai wannan lokacinne jarimi halanchal ya  ce dasu su tafi zuwa gidan da aka tanada na musamman Dan zuwan su birni mai albarka momakon su koma ta cikin wannan kofar da suka shigo sai suka kara nausawa acikin wannan wawa kekiyar pyramid  din bisa kana wannan na'urar mai suffar faranti saida suka kai tsakiyar pyramid din sannan abun yai sama da su basu dau lokaci ba sai gasu a saman pyramid din daga waje sannan abun yai wani irin juyi ya kara biyo jikin ginin pyramid din sai gasu suna yo kasa daga  haka har suka sauka bayan pyramid din daga nanne abun ya tsaya sannan jarimi halanchal ya ce musu mun karaso sai Ku sauko mu tafi nan suka sauko aka kara shiga cikin wani ban gare daban na garin wannan ban garen duk ko ina na'ura ce sama da kasa da  gefe da gefe yanayi wajen ba zai kwatantu ba nafisa ce ta kalli jarimi halanchal tana mai murmushi da wani irin kallo mai dauke da alamun tambaya tana mai cewa jarimi halanchal shin wannan yanki wanne yanki ne acikin yanki burning Khufu jarimi halanchal yace wannan shine yanki duk wasu na urori da wasu masarrafa anan ake sarrafawa duk wani inji da wani Abu Wanda ake kerawa daga wannan unguwar yake futowa Ku biyo ni zuwa cikin wannan dakin don na nuna muku machine din da zakuyi amfani dasu wajen wannan yaki nan suka shiga cikin dakin suna shaga kuwa suka koma asalin yan kauye kasance war cikin dakin wayan su irin manyan gun kinan dinasour ne ako ina ko kuma nace dragon jarimi halanchal ne yace kunga wannan sune naurar dinasour da zaku shiga ciki a lokacin yakin kuma aciki zakuyi yaki to tayaya zamu iya yaki dasu bayan bamu iya tuka suba abunda  noor tace kenan, eh zaku koya ai basu da wahala kunsan mu nan ba duniyar mutane kuke ba to duk zaku koyi yadda ake tuka wannan naurar dinasour din acikin dare daya. kai wannan Wawakeken dakin ni kaina ya burgeni domin ko aduniyar mutane baza asami wani company Wanda ya kai wannan tsaruwa ba Maya da nafisa kuwa tuni sun nutsa acikin dakin suna ta kalle kallen abubuwa da kayayyaki acikin wannan dakin jarimi halanchal ne yace kuzo mu karasa barin da zaku Dan huta kafin lokacin cin abunci yayi sannan sarki yace na fada muku yau unguwar nan zasuyi bikinsu na gargajiya da ake duk shekara idan zakuje yace na rakaku eh zamuje karaf nafisa tace zamu bari muyi wanka mu huta sai mu futo muje ko tana fada tana murmushi shima mayar mata da murmushin yai sannan yace ina jiran Ku in kun gama Ku dannah wannan farin makunni da yake jikin bangon dakin nan ni kuma zanzo yanzu nima zanje gidana nan baya na shirya amma fa duk Wanda zaije wajannan anasa pink din kayane ruwan woda da akwaisu acikin gidan sai Ku saka sai anjima ya fada yana mai juyawa  ya FIta daga cikin ban garen ya nufi nasa alokacinne  malam najib sawiris yace shi xai shiga ya kwanta saboda haka sai sun dawo shikwa yana gida, tam baba sai mundawo abunda noor ta cewa abban nata kenan shikwa ya shiga dakin da yaga an rubuta sunan sa kamar haka najib sawiris kamar haka kuma dakin aya da mayah da noor da nafisa dakinsu daban sannan kuma dakin su Abdul da malik da ayu suma dakin su daban ban tsaya ko ina ba sai dakin su aya inda naji sunawa nafisa tsiya suna cewa wai Ashe ita China za, mutafi  noor tace yar uwa ke kuma Ashe china zamu kai ki irin wannan kashe ido Dana ga kina yiwa jarimi halanchal haka ban San lokacin da kika rainani ba noor toma haram ne don't naso Dan China shiba mutum bane ai dama nasan ni wannan kallon da kike mai nasone inji mayah eh shiyasa ai ke naga kuna wasan buya da ayu dan Allah wai mene shirin yar uwa nafisa ce tai maganar tana mai kara so wa gaban mayah tana dariyar shakiyanci ko bakyason dan nawane hhhhh nafisa tai dariyar shakiyanci sannan tace Dana dai ya gani kuma an bashi nan mayah ta tashi da gudu ta shige bandaki  itakwa aya kawai dariya takeyi mata a haka dai suna yin raha suka gama shiri sannan suka sa kayannan Wanda yasha ado da pink din fulawa sannan suka rufe kansu da wani karamin hijab mai kyau Wanda ya kasance shima pink sunsha ado Wanda ya karfesu kasancewar zubin fatar su irin na mutanan misirawan zamanin dane ba karamin kyau kayan sukai musu ba ni kai na lokacin da suka gama kwalliyar saida na suma tsabar kyawunda sukai sai ka rasa wa cce tafi wata kyau acikinsu a yau ne na gasgata cewar lallai jini jinine ko ta yaya sai ya nuna domin a yau ne kaman nin su ya futo fili sosai  ayanayin salon fuskar su da yanayin yadda hijab ya rufe musu fuska kai kace yan"hudu ne tsabar kama sai dai aya duk ta fisu tsayi da zubin tsarin jiki irin na kykkyawar mace nan suka futo inda suka sami su ayu da Abdul da malik suma irin zubin shigarsu iri daya kai yaya Abdul kayi kyau waye ya nada ma wannan rawanin inji noor kenan lokacin da take karaswa wajen sa shikwa murmushi yake mata yana cewa ni na nada kina mamki kike? dole nai mamaki mana kasan ko a Egypt ba kowa ya iyaba eh na sani amma ni na iya ta yaya ka koya ni kaina ban sani ba ya bata amsa malik ne ya kalli aya yah yah  nayi kyau ko nan aya ta rufe fuskar ta tana murmushi yaya malik kayi kyau sosai ma  to mene na rufe fuska ko dan Na kamaki kina kallona eyye nan kwa aka kwashe da dariya, abun mamaki kawai ganin mayah mukai ta nufi wajen ayu tana mai cewa tunda baka iya nadawa ba sai kai magana a nada ma naga sai wani shiru shiru kakeyi alhalin a labarinka da naji kai ba haka kake ba tana maganane fada fada tana mai nadamai rawanin kowa awajen bude baki yai yana kallon su sukwa ko a jikin su ba abunda ayu yake sai murmushi mai taushi wannan shine abunda yake kara furgita mayah da jin kwaunar sa acikin zuciyar ta to mutafi yaya Abdul noor tace tana mai kama hannunsa sukai gaba koda suka je dai dai wajen wannan madanni sai suka danna sannan suka futo daga cikin gida koda futowar su sai suka tarda jarimi halanchal a bakin kofar gidan yana mai jiransu tun kafin su ka rasa futowa ya tsurawa nafisa ido eh lallai nafisa kyakkyawace fiyeda wacce ta zo a tariyin masarautar Khufu jarimi halanchal abunda jarimi halanchal ya fada azuciyarsa kenan sannan yace musu mu tafi nan yayi gaba suka biyoshi abaya bai zame ko ina ba sai bakin wannan kofar wajen taron koda suka shiga sai suka ga wajen dauke da dunbin jama,a kowa yana harkar gabansa amma koda mutanan wajen hankalinsu yakai kan su aya sai wajen yai tsit ba komai ne yasa wajen yai tsit ba sai yadda suka ga masu kamada sarki Khufu tabbas a birnin Khufu ba Wanda bai San kamannin sarki Khufu ba nan take wani attajirin aljani ya nufo su yana mai cewa lale lale barka da zuwa ya zuriar sarki Khufu Ku tawo ga wajen zaman Ku can domin Ku ake jira za a fara wasan da akeyi duk shekara nan sukaje suka zauna akan wayansu kujeru na alfarma wayanda suka sha ado da zinare da wani table Wanda wasu futulu masu kala kala suna haskawa koda suka zauna bisa kan table din sai kayan jikinsu ya kara sawa wajen table din ya kara kyau  a dai dai wannan lokacinne wani mutum ya futo yana mai cewa yaku jama,ar mutanan yanki unguwar nan dake cikin burnin Khufu kuyi sani cewa zamu fara gudanarda wasannin mu kowa ya shirya a dai dai wannan lokacinne wasu irin madangwalai suka futo daga saman ko wanne table  wannan mutumin ya cigaba da cewa muna so muga masoya na gaskiya duk Wanda yasan shida masoyiyar sa suna kyaunar juna to ya sa hannunsa a jikin wannan naurar madangwalin dake kan table don mu tabbatar nankwa mutane aki tayi wani wajen kaji duka wani wajen kaji mari wani wajen kaji shewa wani wajen kaji fashin kwalba a dai dai wannan lokacinne noor ta sa hannunta Dana abdul don ta tabbatarda soyayyarta wa Abdul nan ta ga alamar 100% nan tai tsalle ta rungumeshi tana ehuuu koda hakan ta faru sai Maya da ayu suma suka gwada daga su sai malik da aya sai kuma nafisa da jarimi halanchal daga haka sai wajen yai tsit kowa na kallon masoyinsa suna soyayya wannan shine abunda ya fara a birnin Khufu bayan an nunawa su malam najib sawiris kayan yakin yayansa

 kai wannan Wawakeken dakin ni kaina ya burgeni domin ko aduniyar mutane baza asami wani company Wanda ya kai wannan tsaruwa ba Maya da nafisa kuwa tuni sun nutsa acikin dakin suna ta kalle kallen abubuwa da kayayyaki acikin wannan dakin jarimi ha...

Oops! This image does not follow our content guidelines. To continue publishing, please remove it or upload a different image.
jinah matar aljan book2 ep1Where stories live. Discover now