ZK ___22

2.1K 194 3
                                    

Yau kusan two weeks kenan, babu gara babu labarinta. Sosai da sosai hakan ya dami Asim, sai dai ya ɓoye maitarsa, be yarda ya nuna mata komai ba. Ya kan yi ƙoƙarin siyo duk wani abu na buƙata wanda za'aci ko ayi amfani da shi a gidan. Sai dai duk tsawon wannan satin biyu Namra a wahale tayi su dan kullum yana manne da ita, bata da wani dogon hutu indai yana gida.

Bayan sun gama cin abinci ya aje Spoon ɗin hannunsa yana sauke ajiyar zuciya. Kallonsa tayi dan ta lura da yadda yanayinsa ya canja.

“Lafiya dai?”

Ya ɗan kalleta kaɗan ya ɗauke kai yana ɗan murmushi, fuskarsa na nuna alamun damuwa.

“Ba komai”

“Haba Hubby ai ni da kai yanzu mun zama ɗaya, ya kamata ace damuwarka ta zama nawa, babu wani ɓoye-ɓoye”

“Wato bana son nayi maganar ne kiyi mata wani ɗauka, wata ƙila ba zaki fahimce ni ba”

“Idan ban fahimce ka, wa kake tunanin zai fahimce ka? A tunanin ka idan ka ɓoye min damuwarka zan jidaɗi ne?”

Tashi yayi daga ginciren da yake ya gyara zamansa yana tsara kalamanta, ta yadda zasu zaunu a ƙwaƙwalwarta.

“Namra ina gudun ki shiga cikin irin rayuwar ta ne, kin min abubuwa da yawa, zuciyana bata da muradi illah na kyautata miki. A kullum tunani ina zan zam sama mana mafita muyi rayuwar jindaɗi, sai dai gaskiya I'm scared”

Sai yayi shiru be ƙarasa ba yana auna yadda kalamansa zasu kamata.
Ita kuma sai ta tambaya zuciyarta cike da shauƙin kalaman nasa.

“Scared of what?”

“Namra ba ni da wani aiki ko sana'ah mai ƙwari da zan iya riƙe ki da ita, ƴan kuɗi dana ke tunanin zasu ishe ni na kama sana'ah da su na kama hanayar gidan nan 50,0000 per year dan kawai na burge ƴan'uwanki da ke kan ki, nasan ke kika bada kuɗin amman naso nayi saving ɗin su dan mu samu wata madafa, sauran da suka rage min kuma gasu muna cin abinci da su kamin Abbah ya yi mana aike”

Ta ɗan ji babu daɗi da kalmar ta fito daga bakinsa, kusan kullum da tunanin take kwana take tashi, na rashin garar da Abbah yayi mata, a tunaninta hakan da Abbah yayi mata ya mata ne dan ta auri Asim, tun da ba haka yake ma sauran ƴaƴansa ba, ita kam ya kasa sai mata girma.

Can ƙasa-ƙasa ta fara magana, zuciyarta cike da rauni.

“Abbah ba zai aiko mana komai ba, da zai aiko da yanzu ya kawo mana ai, sai dai mu yi tunanin wata mafitar”

Sosai da sosai gabansa ya faɗi, kalamanta sun haddasa masa ciwon kai, har zufa na ƙoƙarin karyo masa. Janta yayi jikinsa ya rumgume.

“Toh Allah yayi mana mafita, ai Abbah ya gama mana komai tun da ya yarda na aure ki, Allah dai ya ƙara masa nisan kwana da ƙyaƙƙyawar rayuwa”

“Ameen”

Ta faɗa tana shafa rigarsa.

“Amman yanzu wace sana'ah kake gani yafi? Nifa da zaka bi shawarana da ka koma makaranta, ka cigaba da karatun ka”

“Bana son karatun nan a yanzu kwata-kwata ya fita rai na, na fi son sana'ar da zata riƙa kawo min ƙuɗi sosai ta yadda zan riƙa kyautatawa matana”

“Wace sana'ah zaka yi?”

“Wai da naso na kama wani shago dake nan Uguru Plaza na zuba atamfa haka da lace da shaddodi na gwada na gani, na ma yi maganar shagon dan akwai wani abokina daya ce babansa yana ba da rancen kuɗi ko nawa kake so kayi sana'ah kuna raba riba, toh shine nake son na masa magana”

Ɗagowa tayi ta kalleshi, damuwa ƙarara a fuskarta.

“Kamar nawa zaka kashe?”

“Zai kai 1.5 million, har kuɗin hayar shagon, indai ana son a saka kaya masu kyau”

ZAGON ƘASAWhere stories live. Discover now